Gwamnatin Jihar Kano ta Kaddamar da Kwamitin Gyare-gyare a ma’aikatar Lafiya

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Gwamnatin jihar Kano karkashin jagorancin mai girma gwamna, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ta kaddamar da wani babban kwamiti da aka dorawa alhakin gudanar da muhimman gyare-gyare a ma’aikatar lafiya ta jihar.

An gudanar da bikin kaddamar da kwamitin ne a ofishin sakataren gwamnatin jiha Alhaji Umar Farooq Ibrahim.

IMG 20250415 WA0003
Talla

A wata sanarwa da sakataren yada labaran ofishin sakataren gwamnatin jihar Musa Tanko Muhammad ya Aiko Kadaura24, ya ce wannan matakin ya kara tabbatar da kudirin gwamnatin Kano na karfafawa da farfado da tsarin samar da lafiya a fadin jihar Kano.

Gwamnatin Kano ta magantu kan batun sayawa sarki Sanusi motocin Miliyan 670

An dai dorawa kwamitin alhakin gudanar da cikakken nazari kan kalubalen da ke fuskantar cibiyoyin kiwon lafiya mallakar gwamnati musamman batutuwan da su ka shafi rashin isassun kayan aikin likitanci da kuma gibin da ke tattare da ma’aikata. Aikin na su ya hadar da duk kanana da manya asibitoci dake Kano.

A na sa ran kwamitin zai gabatar da shawarwari masu ma’ana wadanda za su bai wa gwamnati damar samar da ingancciyar kiwon lafiya da daukacin al’ummar jihar Kano.

InShot 20250309 102403344

An bukaci al’umma da masu ruwa da tsaki, da ƙwararru a fannin kiwon lafiya da su ba da gudummawa sosai ga wannan shirin ta hanyar gabatar da shawarwari masu ma’ana ga kwamitin.

Gwamnatin jihar Kano ta nanata kudurinta na sake fasalin fannin kiwon lafiya tare da mutunta irin gudunmawar da masu ruwa da tsaki ke bayarwa wajen gina jihar Kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba Ya Sanya Hannu Kan Dokar Kafa Gaya Polytechnic

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya sanya...

Sojoji sun mikawa Tinubu Shawarwari yadda za a kawo karshen matsalar tsaron Nigeria

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya karɓi rahoton dakarun sojan...

Shugaba Tinubu ya sake nada Buba Marwa a matsayin shugaban NDLEA

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sake tabbatar da nadin...

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa Ya Koma Jam’iyyar APC a Hukumance

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar...