Zargin badakala: Ka fito ka fasa kwan, in ka ki mu fasa maka mugunya- Waiya ga Baffa Bichi

Date:

Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa

 

Gwamnatin Jihar Kano ta kalubalanci tsohon sakataren gwamnatin jiha Dr. Baffa Bichi da ya fito ya bayanan abinda yake da shi wanda aka aikata cin hanci da rashawa ko aikata ba dai-dai ba, tana mai cewa matukar ya gaza fito da hujjoji to ita za ta fito da ta shi badakalar.

“Badakala ce ta sa aka Kore shi daga sakataren gwamnatin jihar Kano, amma saboda kara irin ta mai girma gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya ce a fadawa duniya saboda rashin lafiya aka sallame shi”.

IMG 20250415 WA0003
Talla

Kwamishinan ƴan labarai da harkokin cikin gida na Jihar Kano kwamared Ibrahim Abdullahi Waiya ne ya yi kalubalen a taron manema labarai a nan Kano ranar Juma’a da yamma.

Gwamnatin ta ce tana da bayanai na badakalar kudi da yayi a ayyukan sa a gwamnatin jihar Kano da hukumar Bada tallafin karatu ta gwamnatin tarayya TETFUD wacce hakan ta sa aka kore shi daga aiki.

Rikicin Masarautar kano: Yansanda sun garkame gidan Galadiman Kano

“Kada tsohon sakataren gwamnatin ya manta cewa ba rashin lafiyar sa ne kawai yasa aka kore shi daga sakataren gwamnati ba, harma da badakalar karkatar da Shinkafa da makusantansa su ka yi wanda ana zargin ya na da hannu a ciki,” inji Waiya.

Kwamishinan ya ce matukar Dr. Baffa Bichi da sauran yan jam’iyyar APC na jihar Kano ba su saisaita kalamansa ba, to gwamnatin za ta bankado wasu badakaloli da aka tafka a zamanin mulkin Ganduje.

InShot 20250309 102403344

” A gwamnatin Abba Kabir Yusuf ba bu wasu shafaffu da mai, sabanin gwamnatin Ganduje da shi da mai daukinsa da wasu mutane biyu ne kadai suke iya yanke me za a yi a gwamnatin, sabanin yanzu da ake komai bisa chanchanta”. A cewar Waiya

“Tun da aka kirkiri jihar Kano ba’a taba yin gwamnatin jiha a Kano da ta yi Al’mundahana da wawure dukiyar al’umma kamar gwamnatin APC ta shekaru 8 a jihar Kano ba, Amma wai Baffa Bichi da ya saka yaransa suka wawure dukiyar al’umma shi ne zai ce yana da bayanan da wasu suka aikata ba dai-dai ba,” inji Waiya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba Ya Sanya Hannu Kan Dokar Kafa Gaya Polytechnic

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya sanya...

Sojoji sun mikawa Tinubu Shawarwari yadda za a kawo karshen matsalar tsaron Nigeria

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya karɓi rahoton dakarun sojan...

Shugaba Tinubu ya sake nada Buba Marwa a matsayin shugaban NDLEA

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sake tabbatar da nadin...

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa Ya Koma Jam’iyyar APC a Hukumance

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar...