Rikicin Masarautar kano: Yansanda sun garkame gidan Galadiman Kano

Date:

Kamal Yakubu Ali

 

Rahotanni na tabbatar da cewa jami’an tsaro sun rufe gidan Galadiman Kano da ke unguwar Galadanci a karamar hukumar Gwale.

Wasu mazauna yankin sun bayyana cewa tun cikin daren jiya Alhamis aka hangi jami’an yansanda sun rufe iya kokin Gidan na Galadima.

“Yansandan sun shigo unguwar ne da kusa kimanin karfe 2 na dare, kuma su ka gindawa motocinsu a kofar shiga gidan da kuma sauran muhimmman hanyoyin da za su sada mutum da gidan na Galadiman Kano” . Inji wani mazaunin unguwar

IMG 20250415 WA0003
Talla

Ya ce tun a makon da ya gabata ne sarki Sanusi ya ba da umarnin gyare gidan domin sabon Galadiman da zai nada ya tare a gidan tunda dama gidan sarautar Galadiman Kano ne.

Wannan dai na zuwa ne bayan da ake saran Sarkin Kano Muhammad Sunusi || zai raka Galadiman Kanon da ya nada Mannir Sunusi, bayan na dashi kamar yarda al-adar Masarautar Kano take.

Kungiyar Kwadago ta Kano ta aikewa gwamna Abba gida-gida muhimmin sako

Rikicin Masarautar kano na neman sake dawowa sabo tun bayan mutuwar Galadiman Kano Alhaji Abbas Sanusi, inda Sarki Sanusi II ya nada Munnir Sanusi a matsayin Galadima yayin da shi ma Sarki Aminu Ado Bayero ya nada dan uwansa Alhaji Sanusi Ado Bayero a matsayin Galadima.

InShot 20250309 102403344

Kuma dukkanin wadannan nadin mai cin karo da juna zai gudanar da bukukuwan nadin ne a Wannan rana ta Juma’a, sai Sarki Sanusi za na da na shi Galadiman a fadarsa dake gidan rumfa yayin da Shi kuma Sarki Aminu zai nada na shi Galadiman a fadarsa dake gidan Sarki na Nasarawa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dalibai 22 sun kammala karatu da daraja ta 1 a bikin yaye ɗalibai na farko na Jami’ar Baba-Ahmed Kano

Jami’ar Baba-Ahmed, Kano ta gudanar da bikin yaye ɗalibai...

Rundunar Sojin Amuruka ta kammala tsara yadda za ta kawo wa Nigeria hari

  Rundunar sojin Amurka da ke Afirka, AFRICOM, ta gabatar...

Kalaman Trump: Gwamnatin Nigeria ta Fara tattaunawa da Gwamnatin Amuruka

Gwamnatin Najeriya ta ce a gwamnantance tana tattaunawa da...

Ba zan bar Siyasa ba har lokacin da zan bar Duniya – Mal Shekarau

Tsohon Gwamnan jihar Kano, Malam Ibrahim Shekarau ya ce...