A Gaggauce: Gwamnan Kano ya sanya hannu kan dokokin kirkirar sabbin ma’aikatu 4

Date:

Daga Aliyu Danbala Gwarzo

 

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya sanya hannu kan dokokin kirkirar sabbin ma’aikatu gwamnatin jihar har guda hudu.

Gwannan ya ce kirkirar sabbin ma’aikatun zai kara taimakawa wajen inganta cigaban jihar Kano.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Kano Sanusi Bature Dawakin Tofa ya sanyawa hannu kuma ya aikowa Kadaura24 ranar Juma’a.

InShot 20250309 102403344

Sanarwa ta ce sabbin ma’aikatun da aka sanyawa dokokinsu hannu su ne kamar haka:

1. Kano State Protection Agency (KASPA)

2. Kano State Signage and
Advertisement Agency (KASIAA)

Mawaki Rarara zai angonce da Jaruma Aisha Humairah

3. Kano State Information and Communication Technologies Development Agency (KASITDA)

4. Kano State Small and Medium Enterprises Development Agency (KASMEDA)

Wadannan dokoki sun shiga cikin kunshin dokokin da jihar Kano ta ke da su, wadanda ake da yakinin za su taimaka matuka wajen inganta masana’antu da kula da tallace-tallace da kuma kare mutane da dai sauransu.

IMG 20250415 WA0003
Talla

Gwamna Yusuf ya ce sanya hannu kan dokokin wata gagarumar nasara ce ga gwamnatinsa a kokarinta na samar da cigaba mai dorewa a jihar Kano.

Ya ce sabbin ma’aikatun za su taka muhimmiyar rawa wajen samar da aikin yi ga matasa da jawo hankalin masu zuba hannun jari da dai sauransu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

An Dauke Shaikh Abduljabbar Daga Gidan Yari na Kurmawa Zuwa Wani Wuri – Yan uwansaba

Wani labari da ke yawo a kafafen sada zumunta...

Majalisu na neman sauya lokacin zabuka a Nigeria

Majalisar Dokoki Ta Ƙasa Ta Gabatar Da Kudirin Sauya...

Kungiyar Lauyoyi yan asalin jihar Kano sun mika korafi ga kasashen Amuruka Ingila da UN kan zargin kisan a Tudun Wada

Kungiyar Lauyoyin Yan Asalin Jihar Kano (National Forum of...

Da dumi-dumi: ASUU ta sanar da ranar da zata fara yajin aiki

Shugabancin Kungiyar Malaman Jami’o’i ta Najeriya (ASUU) ta umurci...