APC a Kano ta magantu kan yunkurin Kwankwaso na shiga jam’iyyar

Date:

Shugaban jam’iyyar APC a Kano, Abdullahi Abbas ya yi kira ga jagoran jam’iyyar NNPP na ƙasa, Rabi’u Musa Kwankwaso da kar ya shigo APC da kungiyar siyasar sa mai suna Kwankwasiyya.

Kadaura24 ta rawaito cewa a kwanan nan akwai raɗe-radin mai karfi cewa Kwankwaso, tsohon gwamnan Kano, na shirin sauya sheka zuwa APC.

IMG 20250415 WA0003
Talla

Sai dai kuma da ya ke taron manema labarai a sakatariyar APC ta Kano a yau Juma’a, Abbas ya ce ba ruwan APC da wata ƙungiya ta siyasa cikin jam’iyyar.

Daily Nigerian ta rawaito duk da cewa Abbas bai fadi Kwankwasiyya ba, amma a jawabin nasa ya nuna cewa babu wata kungiya da za ta dake da jam’iyyar siyasa da za a bari ta shigo cikin APC.

Wata kungiya ta bukaci Gwamnan Kano ya dakatar da Shugaban karamar hukumar Gwale

Ya kara da cewa duk masu tururuwar dawowa APC ba za a ki karbar su ba amma sai sun je mazabu su sun yi rijista.

Ya kuma ce dukkanin shugabannin da ke rike shugabancin jam’iyyar a matakai daban-daban a jihar suna nan akan mukaman su.

InShot 20250309 102403344

” Muna sanar da duk wanda yake son shigowa APC cewa kofar mu a bude take, amma ka sani shigowar ka APC ba zai hana a EFCC da ICPC cigaba da bincikarka ba”. Inji Abdullahi Abbas

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Sanata Barau Jibrin ya zama Uban kungiyar tsofaffin yan majalisun Kano

Kungiyar tsofaffin yan majalisu ta kano sun nada mataimakin...

Babu wanda ya hana ni shiga Fadar Shugaban Kasa – Shettima

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya bayyana cewa babu...

Komawar Kwankwaso APC: NNPP ta Kano ta fadi matsayarta

Daga Hafsat Lawan Sheka   Jam’iyyar NNPP ta jihar Kano ta...

Da dumi-dumi: Kamfanin NNPC ya rage farashin man fetur a Nigeria

Kamfanin albarkatun man fetur na Nigeria NNPCL ya rage...