Wata kungiya ta bukaci Gwamnan Kano ya dakatar da Shugaban karamar hukumar Gwale

Date:

Daga Aliyu Danbala Gwarzo

 

Wata kungiya mai zaman kanta mai suna Arewa Solvation Movement ta bukaci gwamnan jihar Kano da majalisar dokokin jihar da su dakatar da Shugaban karamar hukumar Gwale har sai an kammala bincike da ake yi masa a hukumar yaki da masu yiwa tattalin arziki zagon kasa EFCC.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da aka aikowa Kadaura24, mai dauke da sa hannun shugaban kungiyar na kasa Com. Adamu Sa’ad da sakataren kungiyar Shehu Haruna.

IMG 20250415 WA0003
Talla

Sanarwar ta ce kungiyarsu ta dauki wannan matakin ne a kokarinta na kare martaba da kimar Arewacin Nigeria da kuma kokarin ganin an yi daidai.

” Bai kamata a bar mutumin da ake zargi da almundahanar kudade cigaba da shugabantar al’umma ba, don haka mu ke ganin ya kamata a dakatar da shugaban karamar hukumar don a ba da dama a yi bincike yadda ya kamata”.

“Kima da martabar Kano da karamar hukumar Gwale ya na da matukar muhimmanci shi yasa muke kira ga gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf da majalisar dokokin jihar Kano da su kare kimar Kano da Gwale”. Inji sanarwa

InShot 20250309 102403344

Sanarwar ta ce kungiyar Arewa Solvation Movement ba ta da alaka da wata jam’iyyar siyasa, muna wannan fafutuka ne don kare kimar Arewacin Nigeria.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...