Barka da Sallah: Gwamnan Kano ya bukaci yan jihar su rungumi zaman lafiya da adalci

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya mika sakon barka da sallah ga al’ummar Musulmin Kano da kasa baki daya, inda ya bukace su da su cigaba da aiki da dabi’un da suka koya a watan Ramadan.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa ya aikowa Kadaura24, gwamnan ya jaddada muhimmancin cigaba da dabbaka kyawawan dabi’u da tallafawa mabukata da kuma inganta zaman lafiya.

IMG 20250330 WA0005
Sakon Barka da Sallah

Gwamna Yusuf ya tabbatar wa al’ummar Kano kudirin gwamnatinsa na inganta rayuwarsu, ta hanyar tabbatar da ci gaban tattalin arziki, jin dadin jama’a, samar da ababen more rayuwa.

Murtala Sule Garo ya yiwa Kanawa Barka da Sallah

Da yake jawabi game da kisan gillar da aka yi wa ’yan Kano kwanan nan a Jihar Edo, Gwamnan ya nuna matukar alhininsa game da lamarin.

Ya kuma sha alwashin cewa gwamnatinsa ba za ta yi duk mai yiwuwa har sai an gano wadanda suka aikata wannan aika-aika tare da hukunta su.

InShot 20250309 102403344
Talla

Ya bukaci al’ummar Kano da su yi amfani da lokacin bukukuwan don karfafa dankon zumunci da samar da zaman lafiya.

Ya kuma yi kira al’ummar Musulmi da su yi koyi da kyawawan halaye na Annabi Muhammad (Sallallahu Alaihi Wasallam) ta hanyar tabbatar da adalci da gaskiya da tausayi a cikin dukkan mu’amalarsu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...