Kisan Edo: Yansanda sun bayyana adadin mutanen da suka kama

Date:

Rundunar ƴansandan jihar Edo ta sanar da kama mutum 14 da ake zargi suna da hannu a kashe matafiya a ranar Alhamis.

Matafiyan dai sun ratsa ta jihar ne a hanyarsu daga Fatakwal da ke kudancin Najeriya zuwa Kano da ke arewacin ƙasar, inda wasu ƴan sa-kai suka tare su a yankin Uromi bisa zargin masu garkuwa da mutane ne, wanda hakan ya sa mutanen yankin da suka musu aika-aikar.

InShot 20250309 102403344
Talla

A cewar kakakin rundunar ƴansandan jihar Edo, Moses Yamu, ya ce an kama wasu waɗanda ake zargi da hannu a kisan.

Gwamnatin Kano ta yi Allah -wadai da kisan killar da aka yi wa mafarauta a Edo

“A cigaba da bincike da muke yi, zuwa yanzu mun kama mutum 14 da ake zargi suna da hannu, sannan an yi taron gaggawa tsakanin dukkan masu ruwa da tsaki na yankin domin a kwantar da hankalin jama’a,” in ji Yamu a wata sanarwa da ya fitar ranar Juma’a.

Sai dai rundunar ta ƙara da cewa kawo ɗauki da ta yi ne ya taimaka wajen ceto mutum 10 daga cikin matafiyan.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...