Kisan Edo: Yansanda sun bayyana adadin mutanen da suka kama

Date:

Rundunar ƴansandan jihar Edo ta sanar da kama mutum 14 da ake zargi suna da hannu a kashe matafiya a ranar Alhamis.

Matafiyan dai sun ratsa ta jihar ne a hanyarsu daga Fatakwal da ke kudancin Najeriya zuwa Kano da ke arewacin ƙasar, inda wasu ƴan sa-kai suka tare su a yankin Uromi bisa zargin masu garkuwa da mutane ne, wanda hakan ya sa mutanen yankin da suka musu aika-aikar.

InShot 20250309 102403344
Talla

A cewar kakakin rundunar ƴansandan jihar Edo, Moses Yamu, ya ce an kama wasu waɗanda ake zargi da hannu a kisan.

Gwamnatin Kano ta yi Allah -wadai da kisan killar da aka yi wa mafarauta a Edo

“A cigaba da bincike da muke yi, zuwa yanzu mun kama mutum 14 da ake zargi suna da hannu, sannan an yi taron gaggawa tsakanin dukkan masu ruwa da tsaki na yankin domin a kwantar da hankalin jama’a,” in ji Yamu a wata sanarwa da ya fitar ranar Juma’a.

Sai dai rundunar ta ƙara da cewa kawo ɗauki da ta yi ne ya taimaka wajen ceto mutum 10 daga cikin matafiyan.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dr. Kabiru Getso Ya Mika Ta’aziyya Ga Iyalan Buhari

Daga Rahama Umar Gwaru   Tsohon kwamishinan ma'aikatun lafiya da muhalli...

Gwamnatin tarayya ta ayyana Ranar hutu saboda rasuwar Buhari

Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta ayyana Talata, 15 ga watan...

Injiniya Iliyasu Usman Salihu ya zama Jakadan zaman Lafiya na Africa

    Injiniya Ilyasu Uasman Salihu, Manajan Darakta na Sadex Engineering...

Halin da ake ciki game da shirye-shiryen jana’izar Buhari

Gwamnan jihar Katsina, Dikko Radda, ya bayayna cewa sai...