Gobarar Kwalema: Atiku Abubakar ya jajantawa Matawallen Gwagwarwa

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Tsohon mataimakin shugaban kasa Alhaji Atiku Abubakar ya bukaci gwamnatin jihar Kano da gaggauta tallafawa mutane da iftila’in gobarar Kwalema ta shafa don inganta rayuwarsu.

“Ina kira ga gwamnan jihar Kano da ya gaggauta fara gudanar da cikakken bincike kan musabbabin faruwar wannan gobara domin hana afkuwar irin wannan a gaba. Bugu da ƙari, ina kira ga gwamnati da ta ba da agajin gaggawa da tallafi ga wadanda abin ya shafa tare da aiwatar da matakan dakile sake faruwa a nan gaba”.

InShot 20250309 102403344
Talla

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Alhaji Atiku Abubakar ya wallafa a sashin shafinsa na Facebook da safiyar ranar alhamis din nan.

“Na yi matukar bakin ciki da yadda wata gobara ta tashi a wata karamar masana’anta da ake sarrafa kayayyaki da kasuwanci da ke unguwar Dakata a Jihar Kano da safiyar ranar Larabar da ta gabata”.

Iftila’i: Gobara ta Kone Kasuwar Yan Gwan-Gwan da ke Kano

Ina addu’ar duk wadanda suka rasa dukiyoyinsu da rayuwarsu a wannan lamari mai cike da takaici Allah ya mayar musu, Tabbas an yi asarar biliyoyin nairori, wannan babban rashi ne, ba wai ga wadanda abin ya shafa ba, har ma ga daukacin al’umma.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kungiyar Salanta A Yau ta raba kayan Sallah ga marayu sama da 200

A wani yunkuri na taimako da jin-kai ga marayu...

Hukumar Shari’ah ta jihar Kano ta rabauta da Bohal na sama da miliyan 10 daga kungiyar Wamy

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Hukumar Shari'ah ta rabauta da Katafaren...

Sanarwa ta Musamman Daga Gwamnatin Jihar Kano

SANARWA !!! kasancewar ranar Asabar, 29 ga watan Maris, 2025,...

Gwamnatin tarayya ta aiyana ranakun hutun Sallah

Gwamnatin Najeriya ta ayyana ranakun Litinin 31 ga watan...