Ba zaben 2027 ne a gaba na ba – Tinubu

Date:

 

 

Fadar shugaban Najeriya ta bayyana cewa shugaba Bola Tinubu ya mayar da hankali ne ga kyautata rayuwar ƴan ƙasar, amma ba wai ga zaɓen 2027 ba.

Mai taimaka wa shugaban kan harkokin sadarwa, Sunday Dare wanda ya bayyana haka a shafin X ranar Juma’a, ya ce za a ga nasarorin da gwamnatin Tinubu ta cimma zuwa karshen wa’adinsa na mulki, ta yadda ya kawo ci gaba ga ɓangaren tattali arzikin ƙasar.

InShot 20250309 102403344
Talla

Sanarwar ta Mista Dare na zuwa ne a daidai lokacin da turka-turkar siyasa da kuma tsadar rayuwa ke ƙaruwa a ƙasar.

“Tinubu bai damu da babban zaɓen Najeriya na gaba ba. Ya damu ne kawai kan irin ci gaban da zai kawowa ƴan Najeriya,” in ji sanarwar.

Rikicin Masarauta: Gwamnatin Kano ta Bayyana Matsayarta Kan Hukuncin Kotu

Sanarwar ta ƙara da cewa shugaban ya kuma damu kan yadda tsare-tsaren da ya kawo za su haifar da ɗa mai ido.

“Mun ga saukar hauhawar farashi, mun ga kyautatuwar hada-hadar kasuwanni da kuma harkokin shige da fice na kayayyaki,” in ji sanarwar.

Ta kuma ce an samu zuba-jari da ya kai naira biliyan 50, har ma da saukar farashin kayayyaki.

Sai dai ƴan Najeriya na ci gaba da ƙoƙawa dangane da tsadar rayuwa da suka ce manufofin shugaban sun jefa su, musamman ma cire tallafin man fetur da ya yi lokacin rantsuwar kama aiki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta sake maka Ganduje da ya’yansa a gaban Kotu

Gwamnatin jihar Kano ta kai tsohon gwamnan jihar, Dr....

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta koka da kalaman mataimakin gwamnan Kano

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta Najeriya (NANNM) reshen...

Kotu a Kano ta hukunta masu shago saboda zubar da shara a kan titi

Kotun tafi da gidanka da ke Kano ta yanke...

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...