Waiya ya yi ganawar farko da kungiyar Correspondent Chapel ta Kano

Date:

Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa

 

Kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida na jihar Kano, Kwamared Ibrahim Abdullahi Waiya, ya yi ganawarsa ta farko a da kungiyar wakilan kafafen yada labarai reshen jihar Kano.

Da yake jawabi yayin taron, Kwamishinan ya bayyana cewa, manufarsa ita ce tattaunawa da kungiyar don karfafa dankon zumuncin da ke tsakaninsu.

InShot 20250115 195118875
Talla

Waiya ya bayyana wakilan kungiyar a matsayin ’yan jarida masu bin ka’ida da kwarewa wajen gudanar da ayyukansu.

Kwamishinan ya amince da gudunmawar da kungiyar masu aiko da rahotanni ke bayarwa wajen sanar da jama’a ayyukan gwamnati da shirye-shiryenta.

Jimami: Hadimin Gwamnan Kano ya Rasu

A nasa jawabin shugaban kungiyar wakilan kafafen yada labaran reshen ta jihar Kano, Aminu Garko, ya bayyana jin dadinsa bisa yadda kwamishinan ya nuna gamsuwa da irin aiyukan da suke yi wajen fadakar da al’umma kokarin gwamnatin jihar Kano.

20250228 181700

Ya kuma tabbatar wa da Kwamishinan a shirye su ke su hada kai da ma’aikatar wajen yada sahihan bayanai masu inganci ga jama’a bisa ka’idojin aikin jarida.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

2027: Atiku Abubakar ya bayyana matsayarsa game da kasancewarsa a PDP

  Tsohon Mataimakin Shugaban Kasa, Atiku Abubakar, ya musanta rahotannin...

Cikakken Bayani Kan Yan Bindigar da Yansanda Su Ka Kama a Kano

Daga Rahama Umar Kwaru   Rundunar yansanda ta kasa reshen jihar...

Gidauniyar Sheikh Dr. Muhajihid Aminudden ta rabawa magidanta 600 kayan abinchi a Kano

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Gidauniyar Dr. Muhajihid Aminudden ta rabawa...

Gwamna Abba Gida-gida Ya Kaddamar Da Gyaran Hanyoyi 17 A Babban Birnin Kano

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya ƙaddamar da...