Gwamna Abba Gida-gida Ya Kaddamar Da Gyaran Hanyoyi 17 A Babban Birnin Kano

Date:

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya ƙaddamar da aikin tituna 17 a cikin ƙwaryar birnin Kano.

Ya kaddamar da fara aiyukan ne a yau Asabar a shataletalen Club Road a birnin Kano.

InShot 20250115 195118875
Talla

Ya ce aikin wani ɓangare ne na ƙudurin gwamnatin sa na gyaran birnin Kano, inda ya tabbatar da cewa aikin zai bunƙasa harkokin sufuri da kasuwanci da kuma fito da kimar Kano.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Sanusi Bature Dawakin Tofa ya aikowa Kadaura24.

Dan uwan gwamnan Kano ya bar NNPP Kwankwasiyya

Sanarwar ta ce gwamnan ya yi alkawarin za a gudanar da aiki mai inganci wanda al’ummar jihar Kano za su dade suna amfana.

Ya bukaci yan kwangilar da su tabbatar sun yi aiki mai inganci, inda ya ce musu zai rika yi musu ziyarar bazata domin ganin irin aikin da suke gudana, inda ya ba da tabbacin ba zai lamunci aiki da ha’inci ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...