Waiya ya yi ganawar farko da kungiyar Correspondent Chapel ta Kano

Date:

Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa

 

Kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida na jihar Kano, Kwamared Ibrahim Abdullahi Waiya, ya yi ganawarsa ta farko a da kungiyar wakilan kafafen yada labarai reshen jihar Kano.

Da yake jawabi yayin taron, Kwamishinan ya bayyana cewa, manufarsa ita ce tattaunawa da kungiyar don karfafa dankon zumuncin da ke tsakaninsu.

InShot 20250115 195118875
Talla

Waiya ya bayyana wakilan kungiyar a matsayin ’yan jarida masu bin ka’ida da kwarewa wajen gudanar da ayyukansu.

Kwamishinan ya amince da gudunmawar da kungiyar masu aiko da rahotanni ke bayarwa wajen sanar da jama’a ayyukan gwamnati da shirye-shiryenta.

Jimami: Hadimin Gwamnan Kano ya Rasu

A nasa jawabin shugaban kungiyar wakilan kafafen yada labaran reshen ta jihar Kano, Aminu Garko, ya bayyana jin dadinsa bisa yadda kwamishinan ya nuna gamsuwa da irin aiyukan da suke yi wajen fadakar da al’umma kokarin gwamnatin jihar Kano.

20250228 181700

Ya kuma tabbatar wa da Kwamishinan a shirye su ke su hada kai da ma’aikatar wajen yada sahihan bayanai masu inganci ga jama’a bisa ka’idojin aikin jarida.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rasuwar Buhari: Majalisar Nigeria ta dakatar da duk aiyukanta

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Majalisar dokokin Nigeria ta dage zamanta...

Gwamnati ta baiwa ma’aikata hutu saboda rasuwar Muhammad Buhari

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gwamnatin jihar Katsina karkashin gwamna Umar...

Bayan tura Kashim ya taho da gawar Buhari, Tinubu ya ba da umarnin sassauta Tutar Nigeria

Shugaban kasa Bola Tinubu ya bada umarnin ayi kasa...

Yanzu:yanzu: Tsohon shugaban Nigeria Buhari ya rasu

Innalillahi Wa Inna Ilaihi Raji'un!!! Allah yayi wa tsohon shugaban...