2027: Atiku Abubakar ya bayyana matsayarsa game da kasancewarsa a PDP

Date:

 

Tsohon Mataimakin Shugaban Kasa, Atiku Abubakar, ya musanta rahotannin da ke cewa ya bar jam’iyyar PDP.

Dan takarar shugaban kasa na PDP a zaben 2023 ya sake jaddada goyon bayansa ga hadakar jam’iyyun siyasa don kayar da jam’iyyar APC a 2027.

InShot 20250309 102403344
Talla

Daily Trust ta rawaito cewa, a baya-bayan nan, rahotanni daban-daban sun nuna cewa Atiku yana tunanin barin PDP don shirin takarar shugaban kasa a 2027.

Rahotannin sun ce yana shirin komawa jam’iyyar SDP.

Amma a cikin wata sanarwa da ofishin yada labaransa ya fitar a ranar Asabar, an bayyana cewa tsohon mataimakin shugaban kasar na nan a matsayin cikakken mamba na PDP.

Gidauniyar Sheikh Dr. Muhajihid Aminudden ta rabawa magidanta 600 kayan abinchi a Kano

Yayin da yake karyata rahotannin a matsayin “karya tsagwaronta”, ofishin yada labaran ya bukaci ‘yan Najeriya su yi watsi da su.

Ofishin yada labaran ya jaddada cewa Abubakar ya dade yana kira da a hada kawancen jam’iyyun adawa a Najeriya domin cire APC daga mulki a 2027.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: An sanya dokar hana fita a Jigawa

An sanya dokar hana fita a Jihar Jigawa tare...

Gwamnan Kano ya bayyana abun da gwamnatin za ta yi a filin Idi

  Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya sanar...

Ba zaben 2027 ne a gaba na ba – Tinubu

    Fadar shugaban Najeriya ta bayyana cewa shugaba Bola Tinubu...

Rikicin Masarauta: Gwamnatin Kano ta Bayyana Matsayarta Kan Hukuncin Kotu

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Kwamishinan Shari’a na Jihar Kano kuma...