An yabawa kokarin gwamnatin Kano na tantance Kungiyoyi masu zaman kasansu a jihar

Date:

Daga Tijjani Sarki

 

Wasu daga cikin Kungiyoyi masu zaman kasansu sun yaba da matakin da gwamnatin jihar Kano ta dauka na tantance aiyukansu a jihar.

Mataimakin shugaban kungiyar Human Rights Watch and Youth Empowerment Foundation, Nigeria Tijjani Sarki ne ya bayyana hakan Jim kadan bayan da gwamnatin ta kaddamar da kwamitin.

Ya ce tabbas Wannan matakin zai taimka sosai wajen magance wasu matsaloli da ake zargin Kungiyoyi masu zaman kasansu na haifarwa.

InShot 20250115 195118875
Talla

“Idan aka yi la’akari da zargin daukar nauyin taa’addanci da ake yiwa kungiyar raya kasashe ta Amuruka wato USAID , a iya cewa gwamnatin Kano ta yi abun da ya dace a sanda ya dace”.

Ya ce tantancewa da bibiyar aiyukan Kungiyoyin zai taimakawa gwamnatin ta fitar da duk wata kungiya da ta ke gudanar da aiyukan da za su cutar da al’umma ko da a gaba.

Gwamna Abba ya Rantsar da Sabon Sakataren Gwamnatin Kano

Tabbas Gwamnatin jihar Kano ta yi farar dabara, domin in har wannan kwamiti zai gudanar da aikin da aka dora masa to za a fitar da bara gurbi daga cikin Kungiyoyin farar hula a Kano.

A tunanina bai kamata Kungiyoyi masu zaman kasansu a Kano su damu da wannan matakin ba saboda zai taimakawa wajen inganta aiyukan Kungiyoyin na gaske da kuma fidda bara gurbin cikinmu.

Tijjani Sarki

Mataimakin shugaban kungiyar Human Rights Watch and Youth Empowerment Foundation, Nigeria

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kungiyar cigaban Ilimi da gyaran tarbiya ta unguwar zango ta shirya taron kan tarbiyya da tsaro

Daga Rahama Umar Kwaru   Wani Malami a jami'ar Bayero dake...

Gwamnatin Kano ta sanar da Ranar Fara hutun zangon Karatu na 3 ga ɗaliban jihar

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Gwamnatin Jihar Kano ta sanar da...

Gwamnatin Kano za ta fara jiyo ra’ayoyin al’umma kafin gudanar da duk wani aiki a jihar – Bilkisu Indabo

Daga Samira Hassan   Gwamnatin jihar Kano ta sha alwashin nan...

Kwankwaso ya gana da Tinubu a fadar shugaban kasa

Daga Nasiba Rabi'u Yusuf   Tsohon gwamnan jihar Kano, Rabiu Kwankwaso,...