An yabawa kokarin gwamnatin Kano na tantance Kungiyoyi masu zaman kasansu a jihar

Date:

Daga Tijjani Sarki

 

Wasu daga cikin Kungiyoyi masu zaman kasansu sun yaba da matakin da gwamnatin jihar Kano ta dauka na tantance aiyukansu a jihar.

Mataimakin shugaban kungiyar Human Rights Watch and Youth Empowerment Foundation, Nigeria Tijjani Sarki ne ya bayyana hakan Jim kadan bayan da gwamnatin ta kaddamar da kwamitin.

Ya ce tabbas Wannan matakin zai taimka sosai wajen magance wasu matsaloli da ake zargin Kungiyoyi masu zaman kasansu na haifarwa.

InShot 20250115 195118875
Talla

“Idan aka yi la’akari da zargin daukar nauyin taa’addanci da ake yiwa kungiyar raya kasashe ta Amuruka wato USAID , a iya cewa gwamnatin Kano ta yi abun da ya dace a sanda ya dace”.

Ya ce tantancewa da bibiyar aiyukan Kungiyoyin zai taimakawa gwamnatin ta fitar da duk wata kungiya da ta ke gudanar da aiyukan da za su cutar da al’umma ko da a gaba.

Gwamna Abba ya Rantsar da Sabon Sakataren Gwamnatin Kano

Tabbas Gwamnatin jihar Kano ta yi farar dabara, domin in har wannan kwamiti zai gudanar da aikin da aka dora masa to za a fitar da bara gurbi daga cikin Kungiyoyin farar hula a Kano.

A tunanina bai kamata Kungiyoyi masu zaman kasansu a Kano su damu da wannan matakin ba saboda zai taimakawa wajen inganta aiyukan Kungiyoyin na gaske da kuma fidda bara gurbin cikinmu.

Tijjani Sarki

Mataimakin shugaban kungiyar Human Rights Watch and Youth Empowerment Foundation, Nigeria

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...