Majalisar Limaman Masallatan Juma’a ta bayyana goyon bayanta ga matakin gwamnatin na tantance Kungiyoyin farar hula

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Majalisar limaman masallatan Juma’a ta kasa karkashin jagorancin shugabanta Sheikh Muhammad Nasiru Adam, ta bayyana goyon bayanta ga shirin gwamnatin jihar Kano na tantance kungiyoyi masu zaman kansu.

Sheikh Muhammad Nasiru Adam ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Kano ranar Litinin.

Sheikh Muhammad Nasiru Adam shi ne babban limamin masallacin Sheikh Ahmad Tijjani dake kofar mata a tsakiyar birnin Kano.

Sheikh Muhammad Nasiru Adam ya ce “Muna goyon bayan gwamnatin jihar Kano a kan matakin da ta dauka na tantance kungiyoyi masu zaman kansu.”

InShot 20250115 195118875
Talla

Sheikh Muhammad Nasiru Adam ya jaddada mahimmancin tantance kungiyoyi masu zaman kansu, inda ya bayyana cewa wasu ayyukan kungiyoyin sun sabawa al’ada, da addinin mutanen Kano.

Zargin batanci: Kotu ta aikewa Abdullahi Abbas da Faizu Alfindiki sammaci

Ya bayyana cewa wadannan ayyuka a wasu lokuta suna yin illa ga zamantakewar al’ummar Kano.

Sheikh Muhammad Nasiru Adam ya kara da cewa Majalisar Limaman Juma’a ta himmatu wajen aiwatar da ayyukan da suke taimakawa da kuma amfanar addinin Musulunci.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dr. Kabiru Getso Ya Mika Ta’aziyya Ga Iyalan Buhari

Daga Rahama Umar Gwaru   Tsohon kwamishinan ma'aikatun lafiya da muhalli...

Gwamnatin tarayya ta ayyana Ranar hutu saboda rasuwar Buhari

Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta ayyana Talata, 15 ga watan...

Injiniya Iliyasu Usman Salihu ya zama Jakadan zaman Lafiya na Africa

    Injiniya Ilyasu Uasman Salihu, Manajan Darakta na Sadex Engineering...

Halin da ake ciki game da shirye-shiryen jana’izar Buhari

Gwamnan jihar Katsina, Dikko Radda, ya bayayna cewa sai...