Gwamnatin Kano za ta fara jiyo ra’ayoyin al’umma kafin gudanar da duk wani aiki a jihar – Bilkisu Indabo

Date:

Daga Samira Hassan

 

Gwamnatin jihar Kano ta sha alwashin nan gaba kadan za ta fara shiga lungu da sako na kananan hukumomi 44 domin jiyo ra’ayoyin al’umma game da aikin da su ke bukatar gwamnatin ta yi musu a yankunansu.

” Gwamnan jihar Kano ya samar da wannan ofishin nawa ne don mu rika jiyo abubuwan da al’umma su ke bukata mu kai masa shi kuma ya aiwatar don amfanin al’ummar jihar Kano”.

Sabuwar mai baiwa gwamnan Kano Shawara ta musamman kan fadakar da al’umma, Hajiya Bilkisu Yakubu Indabo ce ta bayyana hakan yayin wata ganawa da manema labarai a Kano .

InShot 20250309 102512486
Talla

Ta ce yadda gwamnan kano ya shiga cikin al’umma lokacin da ya ke yakin neman zabe , haka su ma za su shiga cikin al’ummar domin su jiyo abubuwan da su ke bukata don aiwatarwa al’ummar jihar .

” Yanzu haka gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya cika sama da kaso 85 na alkawuran da ya yi wa Kanawa lokacin da ya ke neman kuri’un al’umma , don haka yanzu za mu fara jin aiyukan da al’umma suke bukatar sannan mu gabatarwa gwamnan domin zartar da aiyukan”. Inji Bilkisu Indabo

Kwankwaso ya gana da Tinubu a fadar shugaban kasa

Mai baiwa gwamnan Shawara wacce it ce tsohuwar Kantomar karamar hukumar Wudil ta ce za ta yi aiki tukuru domin ganin ta sauke nauyin da gwamnan Kano ya dora mata don inganta rayuwar al’umma.

Hajiya Bilkisu Yakubu Indabo ta bukaci al’umma jihar Kano su ba ta hadin kan da ya dace don kyautata rayuwar al’ummar jihar Kano dake birni da karkara.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: An tsinci gawar wata dattijuwa mai shekaru 96 cikin rami masai a Kano

A ranar Alhamis al’ummar ƙauyen Sarai da ke ƙaramar...

Na riga Kwankwaso shiga harkokin Siyasa – Sanata Barau Jibrin

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, ya...

Jaridun Amurka sun bankado Tsare-tsare uku da sojojin Amurka ke yi don tunkarar Najeriya

Rahotanni daga wasu jaridun Amurka na bayyana cewa rundunar...

Dalibai 22 sun kammala karatu da daraja ta 1 a bikin yaye ɗalibai na farko na Jami’ar Baba-Ahmed Kano

Jami’ar Baba-Ahmed, Kano ta gudanar da bikin yaye ɗalibai...