Gwamnatin Kano ta Sanya Ranar Rufe Makarantun Firamare da Sakandire

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Gwamnatin jihar Kano ta amince da ranar juma’a 28 ga watan fabarairu, 2025, a matsayin ranar hutun Zango karatu na biyu ga makarantun firamare da sakandire dake jihar baki daya.

A wata sanarwa da daraktan wayar da kan al’umma na ma’aikatar ilimi ta jihar Kano, Balarabe Abdullahi Kiru ya aikewa manema labarai , ya ce hutun ya shafi makarantu masu zaman kansu da na gwamnati .

InShot 20250115 195118875
Talla

Sanarwar ta ce daliban makarantun firamare da sakandire na kwana za su koma Makarantunsu a ranar lahadi 06 ga watan Afirilu,2025, su kuma na makarantun jeka ka dawo za su koma Makarantar ranar litinin 07 ga watan Afirilu, 2025.

Gwamnan Kano ya lashe lambar yabo ta gwamna mafi ƙwazo a Afirka

Kwamishinan ilimi na jihar Kano Dr. Ali Haruna Makoda ya bukaci iyayen yaran da su tabbatar da cewa ya’yansu sun koma Makarantar a ranakun da aka sanya.

Sanarwar ta gargadi masu makarantu masu zaman kasansu da su tabbatar da bin ka’idar da aka gindaya ko kuma su fuskanci hukunci.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...