Zaben 2027: Kwankwaso ya bugi kirji

Date:

Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, tsohon gwamnan jihar Kano, ya ce jam’iyyar NNPP za ta kayar da dukkan jam’iyyun siyasa a zabe mai inganci da adalci.

Kwankwaso ya bayyana haka ne a ranar Alhamis a taron kwamitin zartarwa na kasa (NEC) na jam’iyyar a Abuja.

InShot 20250115 195118875
Talla

Dan takarar NNPP a zaben 2023 din ya soki gwamnatin Bola Tinubu, yana mai cewa ‘yan Najeriya na fuskantar matsin rayuwa fiye da yadda aka taba gani a baya.

“Gaskiya ne da wuya a tuna da wani da ke farin ciki da gwamnatin APC a kowane mataki, musamman a matakin tarayya,” in ji shi.

“‘Yan Najeriya sun shaida wahalhalu da ba a taba gani ba a tarihin wannan kasa.

Dan Majalisar NNPP ya fice daga jam’iyyar zuwa APC

“Talauci ya yadu ko’ina. Mun ga rashin tsaro, gine-gine da ababen more rayuwa suna lalacewa, kuma ba mu ga wani kokari na gyara su ba.

“Na yi imani idan aka gudanar da sahihin zabe a wannan kasa, jam’iyyarmu za ta kayar da APC, PDP da sauran jam’iyyu.”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...