Sha’aban Sharada ya sami sabon mukami

Date:

Daga Sharifiya Abubakar

 

Kungiyar ‘yan majalisun dake kula da tsaro da bayanan sirri ta duniya (PI-SF) ta nada tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano Hon. Sha’aban Ibrahim Sharada, matsayin Daraktan Hulɗa da ‘yan majalisar Afrika kuma memba a kwamitin zartarwa na kungiyar.

Nadin nasa na kunshe ne cikin wata sanarwa da shugaban kungiyar na duniya dan majalisar Amurka Robert Pittenger ya sanyawa hannu ranar 4 ga Fabarairun 2025.

InShot 20250115 195118875
Talla

Sanarwar ta kara da cewa, jajircewa da kuma kwarewarsa wajen bunkasar harkokin tsaro a fadin duniya ya sanya ya zama mafi chanchanta da mukamin.

Dan Majalisar NNPP ya fice daga jam’iyyar zuwa APC

Darakta Sha’aban zai mayarda hankali wajen Inganta hulɗa da haɗin gwiwa tsakanin shugabannin majalisun Afrika don tunkarar matsalolin tsaro da gudanarwa, hadi da kawo ƙarin ‘yan majalisa, jami’an tsaro, da masu tsara manufofi daga Afrika cikin tarukan kungiyar.

Kazalika sabon daraktan zai samar da fagen tattaunawa tare da majalisun Afrika don inganta haɗin kai kan tsaro, leƙen asiri, tsaron yanar gizo, da sauransu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...