Sha’aban Sharada ya sami sabon mukami

Date:

Daga Sharifiya Abubakar

 

Kungiyar ‘yan majalisun dake kula da tsaro da bayanan sirri ta duniya (PI-SF) ta nada tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano Hon. Sha’aban Ibrahim Sharada, matsayin Daraktan Hulɗa da ‘yan majalisar Afrika kuma memba a kwamitin zartarwa na kungiyar.

Nadin nasa na kunshe ne cikin wata sanarwa da shugaban kungiyar na duniya dan majalisar Amurka Robert Pittenger ya sanyawa hannu ranar 4 ga Fabarairun 2025.

InShot 20250115 195118875
Talla

Sanarwar ta kara da cewa, jajircewa da kuma kwarewarsa wajen bunkasar harkokin tsaro a fadin duniya ya sanya ya zama mafi chanchanta da mukamin.

Dan Majalisar NNPP ya fice daga jam’iyyar zuwa APC

Darakta Sha’aban zai mayarda hankali wajen Inganta hulɗa da haɗin gwiwa tsakanin shugabannin majalisun Afrika don tunkarar matsalolin tsaro da gudanarwa, hadi da kawo ƙarin ‘yan majalisa, jami’an tsaro, da masu tsara manufofi daga Afrika cikin tarukan kungiyar.

Kazalika sabon daraktan zai samar da fagen tattaunawa tare da majalisun Afrika don inganta haɗin kai kan tsaro, leƙen asiri, tsaron yanar gizo, da sauransu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Za mu kashe Sama da Naira miliyan 105. Dan Bunkasa Harkar ilimi a karamar hukumar Dala – Hon Surajo Imam

Daga Sani Idris maiwaya   Shugaban karamar hukumar Dala Alhaji Surajo...

Zaben 2027: Kwankwaso ya bugi kirji

Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, tsohon gwamnan jihar Kano, ya...

Dan Majalisar NNPP ya fice daga jam’iyyar zuwa APC

  Yusuf Galambi dan majalisar wakilai ya sauya sheka daga...

Ku ba mu hadin kai mu sauke nauyin da gwamnan Kano ya dora mana – Barr. Dan Almajiri ga mawadata

Daga Kamal Yakubu Ali   Sabon shugaban hukumar zakka da Hubusi...