Majalisar Wakilai ta bukaci Gwamnatin tarayya ta dakatar da karin kudin kiran waya da na data

Date:

Majalisar Wakilan Najeriya ta yi kira ga Ministan Sadarwa da Tattalin Arziki a Fasar Zamani, Bosun Tijani, da Hukumar Sadarwa ta Ƙasa (NCC), da su dakatar da karin kudin kiran waya da na data da ake shirin yi.

Kiran ya biyo bayan amincewa da kudirin gaggawa da dan majalisa Obuku Offorji ya gabatar a zaman majalisar da aka yi ranar Talata.

InShot 20250115 195118875
Talla

Yayin gabatar da kudirin, ya bayyana cewa ministan ya bayyana a ranar Laraba, 8 ga watan Janairu, a wani taron masu ruwa da tsaki, cewa kamfanonin sadarwa za su kara farashin kiran waya da na Data a nan gaba.

A cewarsa, ana ci gaba da tuntuba, domin wasu daga cikin kamfanonin sadarwa suna kokawa kan bukatar karin kudin har zuwa kashi 100 cikin 100.

Hukumar hana cin hanci ta Kano ta kama wani Hadimin Gwamnan Kano

Sai dai ya ce karin ba zai kai kashi 100 cikin 100 ba, kuma NCC za ta amince da sabbin farashin sannan ta sanar da su a lokacin da ya dace.

Sai dai, dan majalisar ya kalubalanci hujjojin da kamfanonin sadarwa suka bayar dangane da karin kudin, wadanda suka hada da kudin saka hannun jari, inganta cibiyoyin sadarwa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...

Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali ta Magantu Kan Batun Sheikh Abduljabbar

Hukumar Gyaran Hali ta Jihar Kano ta bayyana cewa...

Dalilin da ya sa na bar tafiyar Kwankwasiyya – Farouk Lawan

Tsohon ɗan majalisar tarayya, Farouk Lawan, ya bayyana cewa...

An Dauke Shaikh Abduljabbar Daga Gidan Yari na Kurmawa Zuwa Wani Wuri – Yan uwansaba

Wani labari da ke yawo a kafafen sada zumunta...