Majalisar Wakilai ta bukaci Gwamnatin tarayya ta dakatar da karin kudin kiran waya da na data

Date:

Majalisar Wakilan Najeriya ta yi kira ga Ministan Sadarwa da Tattalin Arziki a Fasar Zamani, Bosun Tijani, da Hukumar Sadarwa ta Ƙasa (NCC), da su dakatar da karin kudin kiran waya da na data da ake shirin yi.

Kiran ya biyo bayan amincewa da kudirin gaggawa da dan majalisa Obuku Offorji ya gabatar a zaman majalisar da aka yi ranar Talata.

InShot 20250115 195118875
Talla

Yayin gabatar da kudirin, ya bayyana cewa ministan ya bayyana a ranar Laraba, 8 ga watan Janairu, a wani taron masu ruwa da tsaki, cewa kamfanonin sadarwa za su kara farashin kiran waya da na Data a nan gaba.

A cewarsa, ana ci gaba da tuntuba, domin wasu daga cikin kamfanonin sadarwa suna kokawa kan bukatar karin kudin har zuwa kashi 100 cikin 100.

Hukumar hana cin hanci ta Kano ta kama wani Hadimin Gwamnan Kano

Sai dai ya ce karin ba zai kai kashi 100 cikin 100 ba, kuma NCC za ta amince da sabbin farashin sannan ta sanar da su a lokacin da ya dace.

Sai dai, dan majalisar ya kalubalanci hujjojin da kamfanonin sadarwa suka bayar dangane da karin kudin, wadanda suka hada da kudin saka hannun jari, inganta cibiyoyin sadarwa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin Sarautar Kano: Fadar Sarki Sanusi ta zargi magoya bayan Sarki Aminu Ado Bayero da kai farmaki Kofar Kudu

Daga Sani Idris Maiwaya   Rikicin Masarautar kano ya na neman...

Shugabannin Kasuwar Kanti Kwari sun shiryawa Gwamnan Kano Addu’o’i na musamman

Daga jafar adam Shugaban kasuwar Kantin Kwari Sharu Abdullahi Namalam...

Dalilin Kwankwaso na kin shiga Hadakar ADC

Jam'iyyar NNPP ta ce abin da ya sa ba...