Gwamnatin kano ta ja kunnen yan kwangilar ayyukan kananan hukumomin kano da su tabbatar da sun yi aiki mai inganci kamar yadda su ka yi alkawari na tsawon shekaru 20 tare da gujewa bayar da na goro wajen bibiyar takardun kwangila.
Kwamishinan kananan hukumomin kano Hon Muhammad Tajo Usman ne ya bayyana hakan yayin da ‘yan kwangilar suka kai ziyarar aiki ofishin sa dake ma’aikatar kananan hukumomin kano.
Yana mai cewar, kafin a bayar da wani aiki a gwamnatance, an ajiye kudin da za’a biya ‘dan Kwangila hakkin sa.
![InShot_20250115_195118875 InShot 20250115 195118875](https://kadaura24.com/wp-content/uploads/2025/01/InShot_20250115_195118875-300x298.png)
Ya kara da cewa, ba’a yarda wani dan Kwangila ya dinga zuwa ma’aikatar kananan hukumomi domin bibiyar Fayal dinsa ba domin gudun rashawa a tsakanin ma’aikata da Dan Kwangila.
“Haka kuma akwai sabuwar ma’aikata ta musamman da gwamnatin kano ta Samar da zata dinga bibiyar aikin da aka bayar daga kananan hukumomin kano domin tabbatar da nagartar ayyukan da aka basu – “.inji kwamishinan”
Da yake jawabi ga manema labarai jim kadan bayan fitowar su, Shugaban kungiyar ‘yan kwangilar ayyukan kananan hukumomin kano 44 (Association of 44 local government contractors of Nigeria Kano State Branch) Alhaji Rabiu Aliyu Kiru ya jaddada aniyar su na kora da kuma gurfanar da duk wani Dan Kwangila daga cikin mambobin su da yayi aiki mara Inganci tare da sabunta aikin da aka bashi ba tare da an sake biyan kudin aikin ba.
Ya kara da cewa, tuni dai shirye shirye su ka yi nisa wajen fara ayyukan kananan hukumomin kano 44 domin sabunta jihar kano da manya manyan ayyukan gwamnatin kano.