Da dumi-dumi: Tinubu ya baiwa sakataren jam’iyyar APC na Kano mukami

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Sakataren jam’iyyar APC na jihar Kano, Alhaji Ibrahim Zakari Sarina, ya zama kwamishinan hukumar korafe-korafen jama’a ta kasa (PCC), mai wakiltar jihar Kano.

Sarina ya maye gurbin Hon Yusuf Abdullahi Ata, wanda aka nada shi a matsayin karamin ministan gidaje da raya birane.

 

Ata ya kasance kwamishinan PCC mai wakiltar jihar Kano daga Yuli zuwa Oktoba 2024 kafin shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya nada shi a matsayin minista.

Gwamnatin Kano ta haramtawa yan kwangila zuwa ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar – Kwamishina

Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Obot Akpabio, ne ya sanar da nadin Sarina a zaman na yau.

Sarina, dai yanzu haka shi ne sakataren jam’iyyar APC na jihar Kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...

Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali ta Magantu Kan Batun Sheikh Abduljabbar

Hukumar Gyaran Hali ta Jihar Kano ta bayyana cewa...

Dalilin da ya sa na bar tafiyar Kwankwasiyya – Farouk Lawan

Tsohon ɗan majalisar tarayya, Farouk Lawan, ya bayyana cewa...

An Dauke Shaikh Abduljabbar Daga Gidan Yari na Kurmawa Zuwa Wani Wuri – Yan uwansaba

Wani labari da ke yawo a kafafen sada zumunta...