Sanata Barau zai baiwa dalibai 1,000 tallafin karatu a Kano ta tsakiya da ta Kudu

Date:

Daga Aliyu Danbala Gwarzo

 

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I Jibrin, ya kammala shirye-shiryen bayar da tallafin karatu ga dalibai 1,000 don yin karatun digiri a fannonin da suka shafi fasahar zamani, ICT, ƙarƙashin Gidauniyar Barau I Jibrin, BIJF.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun mai taimakawa Sanatan kan harkokin yada labarai Ismael Muddashi .

InShot 20250115 195118875
Talla

Sanarwar ta ce wadanda za su ci gajiyar shirin su ne daliban da su ka fara karatu a cibiyoyin karatu guda bakwai a Jami’ar Tarayya da ke Dutsin-ma da ke Jihar Katsina da za a kafa a mazabar Kano ta tsakiya da ta Kudu daga Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa.

Ya ce Sanata Barau da mahukuntan jami’ar sun kammala shirye-shiryen kafa cibiyoyin karatu a mazabun biyu.

Matasan da Barau Jibrin ya dauki nauyin karantunsu sun bar Kano zuwa India

Sanata Barau Jibrin ya dauki wannan matakin ne a kokarinsa na tallafawa matasa Maza da mata don inganta rayuwarsu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kotu a Kano ta hukunta masu shago saboda zubar da shara a kan titi

Kotun tafi da gidanka da ke Kano ta yanke...

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...

Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali ta Magantu Kan Batun Sheikh Abduljabbar

Hukumar Gyaran Hali ta Jihar Kano ta bayyana cewa...

Dalilin da ya sa na bar tafiyar Kwankwasiyya – Farouk Lawan

Tsohon ɗan majalisar tarayya, Farouk Lawan, ya bayyana cewa...