Gwamnatin Kano za ta ginawa masu lalurar laka cibiyar fasahar sadarwa

Date:

Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa

 

Gwamnatin jihar Kano ta jaddada Kudirinta na tallafawa masu bukata ta musamman, musamman masu lalurar laka domin inganta rayuwarsu.

Kwamishinan yada labarai na jihar Kano Kwamared Ibrahim Abdullahi Waiya ne ya bayyana hakan yayin rabon kayan tallafi da kungiyar masu fama da lalurar laka ta baiwa ya’yan kungiyar da hadin gwiwar gidauniyar MacArthur.

InShot 20250115 195118875
Talla

Kwamishina Waiya ya ce yana da muhimmanci a tallafawa masu fama da lalurar laka saboda mawuyacin halin da suke ciki sakamakon lalurar da kuma iyalansu.

Ya ba su tabbacin gwamnatin jihar Kano za ta cigaba da fito da tallafin don ingantawa masu lalurar.

Yaki da Azzalumai: Gwamnan Kano Abba Gida Gida Ya Zare Takobi a Garin Zarewa

Kwamishinan ya ce gwamnatin Kano za ta hada hannu da kungiyar domin samar da cibiyar fasahar sanarwa, sannan a sanya musu kayan aikin a koya musu don inganta rayuwarsu.

A wata sanarwa da daraktan aiyuka na musamman na ma’aikatar yada labarai Sani Abba Yola ya aikowa Kadaura24, ya ce Waiya ya yabawa iyalan wasu lalurar saboda yadda suke tallafawa yan uwansu, sannan ya ba su tabbacin gwamnatin jihar Kano zata cigaba da tallafawa musu don saukaka musu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...