Tinubu ya ba da umarnin a baiwa Kwankwaso, Bichi da sauran wadanda ya nada takardun kama aiki

Date:

Daga Maryam Muhammad Ibrahim

 

Shugaban Kasa Bola Ahmad Tinubu ya ba da umarnin a gaggauta sakin takardar nadin mukamin da aka yiwa Musa Iliyasu Kwankwaso, Rabi’u Sulaiman Bichi da sauran mutane 10 da aka nada su domin jagorantar hukumomin raya kogunan kasar nan 12 .

Idan za a iya tunawa Kadaura24 ta rawaito a ranar 18 ga watan disambar shekarar da ta wuce shugaban Kasa Bola Ahmad Tinubu ya amince da nada su domin jagorantar hukumomin raya kogunan kasar nan dake karkashin ma’aikatar ruwa ta Kasa.

InShot 20250115 195118875
Talla

Shugaba Tinubu ya bayar da umarnin ne bayan wani rahoto na musamman da jaridar Tribune ta yi, kan rashin baiwa wadanda aka nadin takardar nadin mukamin da aka yi musu sama da wata daya da ya gabata.

Jaafar Jaafar ya fallasa sunan mai kitsawa gwamnatin Kano makarkashiya a Abuja

Rahotanni sun nuna cewa an rike takardaun ne bisa wasu dalilai da har yanzu ba a bayyana nasu ba, amma dai ana zargin suna da nasaba da Siyasa.

 

Rahotanni sun nuna cewa wadanda aka ki baiwa takardun kama Aikin sun yi niyyar fara aiki a makon da ya gabata duk kuwa da cewa ba a basu takardar shaidar kana aikin ba.

Kwankwaso ya yi zazzafan martani ga rundunar yansada kan Maulidin Inyass na Kano

Sun dai dauki Wannan matakin ne sakamakon wani umarni da aka basu na su je sun kama aiki daga ma’aikatar ruwa ta Kasa, inda aka ce musu za a cigaba da bibiyar lamarin idan suka kama aiki.

A wata wasika mai dauke da kwanan watan 14 ga watan janairu, 2025 da ta fito daga ma’aikatar ruwa kuma aka aikawa sabbin Shugabannin hukumomin raya kogunan, an umarce su da su je su fara aiki in yaso daga baya sai su karbi takardunsu na kama aiki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi Dangote ya sake rage farashin man fetur a Nigeria

Daga Rahama Umar Kwaru   Matatar mai ta Dangote ta bayyana...

Akwai bukatar kebe rana ta musamman a matsayin ranar tsofaffin dalibai a Kano – Kwamared Waiya

Kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida, Kwamared Ibrahim...

Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Daga Aminu Gama   Kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a...

Abubuwan da aka tattauna tsakanin Peter Obi da Gwamnan Bauchi Bala Muhammad

Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya ce a...