Jaafar Jaafar ya fallasa sunan mai kitsawa gwamnatin Kano makarkashiya a Abuja

Date:

Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa

 

Mamallakin jaridar Daily Nigerian Jafar Jafar ya ce mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata Barau Jibrin ne ya yake shirya duk wata makarkashiyar da ake yiwa gwamnatin jihar Kano a Abuja.

” Akwai bayanan sirri da muke samu wadanda suke tabbatar da cewa Sanata Barau Jibrin shi ne yake hada duk wadannan abubuwan ba kamar yadda ake zargin shugaban Jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Umar Ganduje ba”.

Jaafar Jaafar ya bayyana hakan ne cikin wani shiri da suke gabatarwa a kafafen sada zumunta mai suna Fashin Baki.

InShot 20250115 195118875
Talla

Ya ce suna da kunnuwa da tawa don haka suna sami labarai ta karshin kasa, wadanda suke nuna cewa Sanata Barau shi yake amfani da damarsa a gwamnatin tarayya suke kawo wa gwamnatin jihar Kano cikas a duk wani abu da ta shirya gudanarwa.

” Wallahi Ina da kyakykyawar alaka da Sanata Barau Jibrin, amma kuma hakan ba zai hana in fadi gaskiya akan abubuwan da yake yi ba, domin wadannan abubuwan cutar da Kano suke yi”. Inji Jaafar

Gwamnatin Kano Za Ta Fara Shirin Yiwa Ali Madakin Gini Kiranye

Ya ce ya kamata Barau Jibrin ya sani cewa duk abun da yake yi yana yi ne saboda yana so ya mulki garin, ” To idan garin ya lalace ko Allah ya sa ka zama gwamnan Kano abun zai cutar da kai”.

Jaafar Jaafar dai na tsokaci ne kan abun da ya faru na kokarin hana Sarki Sanusi gudanar da taron Maulidin Shehu Ibrahim Inyass da aka yi a Kano ranar asabar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...