Gwamnatin Kano Za Ta Fara Shirin Yiwa Ali Madakin Gini Kiranye

Date:

Kwamishinan yada labarai na jihar Kano Kwamared Ibrahim Abdullahi Waiya ya ce zai jagoranci yiwa dan majalisarsu na tarayya Hon. Ali Sani Madakin Gini kiranye daga Majalisar , sakamakon al’ummar karamar Hukumar Dala da Kano basa bukatar wakilcinsa.

Kadaura24 ta rawaito Kwamared Waiya ya bayyana haka ne yayin taron masu ruwa da tsaki na karamar Hukumar Dala da Yan jamiyyar NNPP, Wanda aka gudanar a dakin taro na Mumbayya dake nan Kano.

InShot 20250115 195118875
Talla

Ya ce karamar Hukumar Dala tana bukatar jagora jajirtacce Wanda zai Kai matsalolin al’ummar yakin Majalisar wakilai domin a magance su.

Kaso 9.6% na daliban firamare a Kano suka iya karatu – UNICEF

Kwamishinan ya kuma godewa Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf bisa tarin mukaman da ya baiwa wadanda suka fito daga karamar hukumar Dala.

Taron ya samu halartar Shugabannin jam’iyyar NNPP na karamar Hukumar Dala da sauran masu ruwa da tsaki na tafiyar Kwankwasiyya a karamar hukumar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: Tinubu ya Iso Kano domin ta’aziyyar Dantata

Shugaban Nigeria Bola Ahmad Tinubu ya iso jihar Kano...

ALGON ta Kano Sa’adatu Soja ta sami sabon matsayi a kungiyar ALGON ta Ƙasa

Daga: Aliyu Danbala Gwarzo. Shugabar karamar hukumar Tudunwada kuma ALGON...

Da dumi-dumi: Tinubu zai zo Kano

Shugaban Kasa Bola Ahmad Tinubu zai zo Kano ranar...

Tinubu ya sauya sunan jami’ar Maiduguri zuwa Sunan Muhd Buhari

Shugaba Bola Tinubu ya sauya sunan Jami'ar Maiduguri zuwa...