Gwamnatin Kano ta yi watsi da yunkurin yan sanda na hana taron Maulidin Shehu Inyass

Date:

Gwamnatin jihar Kano tayi kira ga Shugaban Kasa Bola Tinubu daya bayar da umarnin janye jami’an yan’ sanda da aka jibge a filin wasa na Sani Abacha.

Kwamishinan yada labarai Kwamaret Ibrahim Waiyya ya bayyana hakan yayin wani taron manema labarai.

Kwamared Ibrahim Abdullahi Waiya ya bayyana cewar za’a gudanar da taron Mauludi kamar yadda aka saba gudanarwa a duk shekara.

InShot 20250115 195118875
Talla

Kwamishinan ya kara da cewar babu wani dalili da za ‘a hana mabiya darikar Tijjaniyya gudanar da taron su a gobe kamar yadda aka shirya.

Da dumi-dumi: Yan sanda sun kama Muhuyi Magaji Rimin gadon

Yakara da cewar idan akwai batun rade-raden matsalar tsaro kama yayi Gwamnatin Tarayya ta tun-tunbi gwamnatin Kano, ba kawai a kawo yan’ sanda ba.

Idan za a iya tunawa a wannan rana ta Juma’a rundunar yan sandan Kano ta fitar da sanarwa inda ta ce akwai barazanar tsaro a jihar da kuma wani kulli da suka gano na kai hari jihar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...