Da dumi-dumi: Baffa Babba ya yiwa Kofa Martani Kan sulhunta Kwankwaso da Ganduje

Date:

Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa

 

Shugaban hukumar ingantuwar aiyuka ta Kasa Baffa Babba Danagundi ya ce yana goyon bayan kalaman da dan majalisar tarayya mai wakiltar kananan hukumomin Kiru da Bebeji Abdulmumin Jibrin Kofa ya yi na nema a sulhunta Ganduje da Kwankwaso.

Idan za a iya tunawa Kadaura24 ta rawaito Abdulmumin Jibrin Kofa ya ce ya zama dole su sulhunta Ganduje da Kwankwaso domin cigaban jihar Kano.

Baffa Danagundi ya ce batun da kofa ya zo da shi, batu ne da ya kamata a marasa masa baya domin cigaban jihar Kano.

InShot 20250115 195118875
Talla

Sai dai ya ce akwai bukatar a fadada batun a hada da Shekarau da Kabiru Gaya domin su ma tsofaffin gwamnoni ne da suke da gudunmawar da za su bayar wajen cigaban jihar Kano.

Dangote ya kara farashin man fetur a Nigeria

” Tabbas duk wani mai kishin cigaban Kano dole ya goyi bayan wannan batu na Kofa, Muna goyon bayanka kuma za mu baka duk wani goyon baya domin tabbatar da wannan sulhu tsakanin Kwankwaso da Ganduje da Shekarau da Kabiru Gaya”. Inji Baffa Babba

Baffa Babba Danagundi ya ce ya yi mamakin yadda gwamnan Kano ya dauko batun samar da majalisar tsofaffin gwamnonin Kano domin a rika tattaunawa don cigaban jihar Kano, amma ya fasa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...