Da dumi-dumi: Baffa Babba ya yiwa Kofa Martani Kan sulhunta Kwankwaso da Ganduje

Date:

Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa

 

Shugaban hukumar ingantuwar aiyuka ta Kasa Baffa Babba Danagundi ya ce yana goyon bayan kalaman da dan majalisar tarayya mai wakiltar kananan hukumomin Kiru da Bebeji Abdulmumin Jibrin Kofa ya yi na nema a sulhunta Ganduje da Kwankwaso.

Idan za a iya tunawa Kadaura24 ta rawaito Abdulmumin Jibrin Kofa ya ce ya zama dole su sulhunta Ganduje da Kwankwaso domin cigaban jihar Kano.

Baffa Danagundi ya ce batun da kofa ya zo da shi, batu ne da ya kamata a marasa masa baya domin cigaban jihar Kano.

InShot 20250115 195118875
Talla

Sai dai ya ce akwai bukatar a fadada batun a hada da Shekarau da Kabiru Gaya domin su ma tsofaffin gwamnoni ne da suke da gudunmawar da za su bayar wajen cigaban jihar Kano.

Dangote ya kara farashin man fetur a Nigeria

” Tabbas duk wani mai kishin cigaban Kano dole ya goyi bayan wannan batu na Kofa, Muna goyon bayanka kuma za mu baka duk wani goyon baya domin tabbatar da wannan sulhu tsakanin Kwankwaso da Ganduje da Shekarau da Kabiru Gaya”. Inji Baffa Babba

Baffa Babba Danagundi ya ce ya yi mamakin yadda gwamnan Kano ya dauko batun samar da majalisar tsofaffin gwamnonin Kano domin a rika tattaunawa don cigaban jihar Kano, amma ya fasa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba Ya Sanya Hannu Kan Dokar Kafa Gaya Polytechnic

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya sanya...

Sojoji sun mikawa Tinubu Shawarwari yadda za a kawo karshen matsalar tsaron Nigeria

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya karɓi rahoton dakarun sojan...

Shugaba Tinubu ya sake nada Buba Marwa a matsayin shugaban NDLEA

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sake tabbatar da nadin...

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa Ya Koma Jam’iyyar APC a Hukumance

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar...