Batun kara farashin man fetur a Nigeria ba gaskiya ba ne – IPMAN

Date:

Kungiyar Dillalan Man Fetur ta Nijeriya IPMAN, ta musanta jita-jitar da ake yaɗawa ta ƙarin farashin litar man fetur a faɗin ƙasar.

IPMAN ta ce, yanzu matatun man ƙasar na aiki, kuma hakan zai sa farashin litar man fetur ya ci gaba da sauka.

A tattaunawarsa da Muryar Amurka, Shugaban IPMAN reshen Arewa maso Yamma, Bashir Salisu Tahir, ya musanta wannan zargi na karin farashin litar man fetur.

InShot 20250115 195118875
Talla

Ya kuma tabbatar da cewa babu wani mamban ƙungiyarsu da ya ƙara farashin litar man fetur a ƙasar.

Tahir, ya ce “yanzu kasuwa ce ke samarwa kanta farashi, kuma batun ƙarin farashin litar man fetur a ƙasar babu shi.”

Hajin bana: Hukumar jin dadi alhazai ta Kano ta zamo zakara bisa samun yawan maniyata

Shugaban na IPMAN ya ƙara da cewa “duk da cewa an samu ƙarin farashin man dizel a ‘yan kwanakin nan, farashin sa ne ya tashi a kasuwa, kuma idan farashinsa ya sauko, to tilas za a sayar da shi a farashi me sauki.”

Tahir, ya kara da cewa “yanzu matatun man kasar sun fara aiki, don haka farashin man fetur zai sauko.”

Kawo yanzu dai ’yan Nijeriya na ci gaba da hanƙoron ganin matakan da gwamnati ke ɗauka za su kawo musu sauƙin rayuwar da janye tallafin man fetur ya jefa su a ciki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kansila a K/H Garum Mallam ya rabawa marayu 300 kayan Sallah

Daga Safiyanu Dantala Jobawa   Sama da yara mayaru 300 ne...

Sallah: Baffa Babba ya raba buhu 2,000 na Shinkafa ga Kungiyoyin Tinubu a Kano

Babban daraktan cibiyar kula da ingantuwar aiyuka ta kasa...

Babbar Sallah : Kansilan Lajawa ya raba Naira dubu 500 ga al’ummar mazabarsa

Daga Nura Adam   Kansilan mazabar Lajawa a karamar hukumar Wudil...