Dubun wani matashi da ya sace yaro dan shekaru 2 ta cike a Kano

Date:

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kano, sun kama wani matashi mai shekaru 25, kan zargin sace wani yaro ɗan shekara biyu a duniya, Al’amin Ahmad Garba, tare da neman kuɗin fansa Naira miliyan 50.

Kakakin rundunar ’yan sandan jihar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya ce an kama wanda ake zargin ne a ranar 25 ga watan Disamban 2024.

Talla

An gano yaron a wani gida da ke unguwar Dorayi bayan ya shafe kwanaki uku a ɓoye.

Bayan an ceto yaron, an kai shi Asibitin Ƙwararru na Murtala Muhammad don duba lafiyarsa, sannan aka miƙa shi ga iyayensa.

Dalilin da yasa za a fuskanci katsewar wutar lantarki na akalla sati biyu a Abuja

An gurfanar da wanda ake zargin a kotun majistare mai lamba 25 da ke Nomansland, a Kano.

Kakakin ya ce matashin yanzu haka yana tsare a hannun hukuma, yayin da ake ci gaba da shari’a.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

An Dauke Shaikh Abduljabbar Daga Gidan Yari na Kurmawa Zuwa Wani Wuri – Yan uwansaba

Wani labari da ke yawo a kafafen sada zumunta...

Majalisu na neman sauya lokacin zabuka a Nigeria

Majalisar Dokoki Ta Ƙasa Ta Gabatar Da Kudirin Sauya...

Kungiyar Lauyoyi yan asalin jihar Kano sun mika korafi ga kasashen Amuruka Ingila da UN kan zargin kisan a Tudun Wada

Kungiyar Lauyoyin Yan Asalin Jihar Kano (National Forum of...

Da dumi-dumi: ASUU ta sanar da ranar da zata fara yajin aiki

Shugabancin Kungiyar Malaman Jami’o’i ta Najeriya (ASUU) ta umurci...