Yan Nigeriya sun shiga halin rashin tabbas da yan majalisa suka rera wakar Tinubu

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Al’ummar Nigeria sun shiga ruɗani tun lokacin da suka jiyo yan majalisar tarayya da na Dattawa suna rera taken Tinubu ” Tinubu Anthem” lokacin da shugaban ƙasa Bola Tinubu ya tashi domin gabatar da jawabinsa gabanin gabatar da kasafin kudin shekara ta 2025.

Taken Tinubu wato “Tinubu Anthem” wani take ne da yan Siyasa masu goyon bayan tafiyar Tinubu suke yi musamman idan an zo taron siyasarsu.

Talla

A wani faifen bidiyo na zaman majalisun biyu da jaridar Kadaura24 ta gani, mun jiyo yan majalisar na rera wakar da ke nuna cewa za su tsaya akan duk abun da Tinubu ya umarce su tare da kare muradunsa.

Gwamna Kano ya kara mutum 1 cikin kwamishinonin da Majalisa ta tantance

Abun da yan majalisar su ka yi yasa shakku a zukatan wasu daga cikin al’ummar Nigeriya, musamman game da makomar kasar da yan ƙasar.

A wannan rana ce dai Shugaban ƙasa Bola Tinubu ya gabatar da kasafin kudin shekara ta 2025 ga hadakar majalisar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...