Sanata Kawu Sumaila ya Bayyana Dalilin Alakarsa da Jam’iyyar APC a Yanzu

Date:

Sanatan Kano ta Kudu Sulaiman Abdurrahman Kawu Sumaila ya bayyana cewa jagoran tafiyar Kwankwasiyya Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ne ya kulla alakar dake tsakaninsu da jam’iyyar APC.

Idan za a iya tunawa kadaura24 ta rawaito mabiyan Kwankwasiyya suna ta sukar Kawu Sumaila tare da zargin cewa yana da alaka da yan Jam’iyyar APC saboda yana so ya bar tafiyar su ta Kwankwasiyya a jam’iyyarsu ta NNPP.

A wata hira da yayi da manema labarai a Kano, Sanata Kawu Sumaila yace akan Kujerar Abba Gida Gida, sunje duk inda ake zuwa don neman ayi musu adalci.

Talla

Yace Kwankwaso ne ya kira su (yan majalisar tarayya) ya ja hankalinsu akan su hadu waje guda domin tunkarar duk wanda ya kamata domin a tabbatar da Kujerar gwamnan Kano.

“Jagora Rabi’u Musa Kwankwaso ne ya kirawo mu gidansa , ya yi mana magana ta jagora da mabiya ya ce ya zama dole mu dunkule wurin guda mu je duk inda za mu don ganin ba a kwacewa Abba Kabir Yusuf kurarsa ta gwamnan jihar Kano ba”. Inji Sen. Kawu

Gwamnatin Kano ta tallafawa mata 200 musu lalurar yoyon fitari da Jarin dogaro da kai

Sanata Kawu Sumaila”ya ce ni da Abdullahi Sani Rogo da Abdulmumini Jibrin Kofa Mun ta shi mun nuna masa matsalar shiga cikin maganar amma ya dage sai Mun yi abun da ya fada, sannan ya kawo mana dalilai da hujjojin da har suka sanya muka gamsu da abun da ya zo da shi”.

Sai dai yace ko kusa ko alama, shi a saninsa jam’iyyar NNPP bata shirya wani magudin zabe a lokacin babban zaben shekarar 2023 ba, domin tare dashi aka yi komai na yakin neman

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...