Majalisar Shura ta Darikar Tijjaniyya ta yabawa Gwamnan Kano bisa Nadin Habib Dan almajiri

Date:

Daga Kamal Yakubu Ali

 

Shugaban majalisar shura na Darikar Tijjaniyya ta kasa Khalifa sheikh sani shehu maihula ya yabawa gwamnan jihar kano Alhaji Abba Kabir Yusuf bisa nadin da ya yiwa Sakataren Majalisar Shura ta Darikar Tijjaniyya na kasa Barrister Imam Sheikh Habibu Muhammad Dan Almajiri fagge a Matsayin sabon shugaban hukumar Zakka da Hubusi ta jihar kano .

” A madadin daukacin mabiya darikar Tijjaniyya Muna godiya gwamnan Kano bisa yadda ya zabo daya daga cikinmu ya bashi wannan muhimmin aiki na tarawa da rana zakka ga masu Karamin karfi dake cikin al’umma”.

Talla

 

Shugaban Majalisar Shurar ya bayyana hakan ne cikin wata sanarwa da ya aikowa Jaridar Kadaura24 a ranar juma’a.

Sheikh Khalifa sani mai hula yace hakika an ajiye kwarya a gurbinta, duba da irin gagarumar gudunmawar da Barr. Dan almajiri ya ke baiwa al’umma ,inda ya bayyana barrister Dan àlmajiri a matsayin jajirtacce wajan gudanar da ayukansa ba tare da nuna gazawa ba.

Da dumi-dumi: Gwamnan Kano ya sake baiwa sagagi mukami tare da sabbin nade-nade

Khalifa sani shehu maihula ya bukaci gwamnatin jihar kano data bashi goyan bayan da ya dace domin ganin ya dawo da martaba hukumar, kasancewarsa gogagge wanda ya saba gudanar da muamaloli da mutane daban-daban a fannoni na rayuwar .

A karshe ya yi addu’ar ga barrister Dan almajir ya kuma yi masa fatan sauke nauyin da aka dora masa da kuma neman taimakon ubangiji a yayin gudanarda ayyukansa .
.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

“BAMA YI”: Kalma mai alamta tsayuwar alkiyamar raggo ko mutakabirin dansiyasa – Dr. Murtala Iliyasu Ayagi

  Daga Dr. Murtala Iliyasu Ayagi malamin a Kwalejin Koyar...

2027: Tinubu ya bayyana lokacin da zai ambata sunan wanda zai yi masa mataimaki

I'mFadar Shugaban Kasa ta ce shugaba Bola Tinubu zai...

Ciyaman din Wudil ya kaddamar da aikin gina magudanan ruwa a wasu garuruwa a yankin

Daga Maryam Adamu Mustapha   Shugaban karamar hukumar Wudil, Hon. Abba...