Gwamnati ta dakatar da wani malami saboda wa’azi irin na Boko Haram

Date:

Gwamnatin jihar Neja ta ce za ta gabatar da rahoto ga jami’an tsaro domin su ci gaba da bincike kan wani malamin addini musulunci da ta dakatar bayan zargin sa da yaɗa ‘aƙidar Boko Haram’.

Shugaban Hukumar lura da al’amuran addinai ta jihar Neja, Umar Faruk ya shaida wa BBC cewa an dakatar da malamin ne bayan binciken da gwamnatin jihar Neja ta yi a kansa.

Ya ce “kwamitin da muka kafa ya kira shi kuma mun tattauna da shi, mun gano cewa bai ma yi karatu ba.”

Talla

A cewar sa malamin na gudanar da ayyukansa a garin Tafa da ke jihar Neja, inda ya mallaki Islamiyya kuma yana da mabiya wadanda ke halartar darussansa.

“Da muka lura cewa tafiyarsa da aƙidarsa da da’awarsa akwai hatsari ga tsaron jihar Neja da tsaron kasa, shi ne muka yanke hukuncin cewa a dakatar da shi kuma a rufe makarantarsa har sai jami’an tsaro sun yi bincike a kansa,” in ji Sheikh Faruk.

Ce-ce ku-ce ta barke bayan da mataimakin shugaban kasa ya ambaci Sarki Sanusi II a matsayin Sarkin kano

Ya ƙara da cewa malamin yana kira ne ga magoya bayan sa da su ƙaurace wa zaɓuka da duk wani abin da ya shafi dimokuraɗiyya.

Najeriya dai ta kwashe sama da shekara 10 tana fama da matsalar mayaƙan Boko Haram waɗanda suka addabi arewa maso gabashin Najeriya da kuma wasu ƙasashen yammacin nahiyar Afirka.

Haka nan ƙasar na fama da matsaloli na ƴan fashin daji masu garkuwa da kisan mutane a arewa maso yammacin ƙasar.

Dama dai malamin ya riƙa janyo cece-ku-ce a yankin arewacin Najeriya sanadiyyar kalaman da ya riƙa furtawa kan malaman addinin Musulunci da dama na yankin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...