Gidauniyar Najashi ta Tallafawa Mata Sama da 100 da Jari da kuma Takardun Daukar Aiki

Date:

Da Safiyar ranar Litinin Engr.Alh. Najashi Uba Ismail Gaya, wato MD UIG Oil and Gas ya kaddamar da shirin tallafawa mata Iyayen marayu da jari da kuma mika takardar daukar aiki ga Wasu matan masu kula da asibiti.

Da yake jawabi ga matan bayan raba musu jarin, Alh. Najashi ya ce ya basu jari ne domin su kula da kasu da kuma marayun dake hannun su. Ya kara da cewa wannan shirin kadan ne daga cikin irin aiyuka da wannan Gidauniya zata dinga gabatarwa lokaci bayan lokaci.

Alh. Najashi ya kuma bukaci mutanen da su ka amfana da tallafin da su yi amfani da shi ta hanyar da ta dace Sannan su rika sanya shi acikin addu’o’insu.

Talla

A nasa jawabin Wakiin Sarkin Gaya, ya bukaci sauran mawadata a yankin da su yi koyo da wannan abun alkhairin da Alhaji Najashi ya yi, don rage yawan mabarata da samar da aiyukan yi don bunkasa tattalin arzikin yankin.

Shi wa wakilin Gwamnan kano a wajen taron cewa ya yi, wannan Shiri ya yi dai dai-dai da manufofin Gwamnatin Kano karkashin jagorancin Alh. Abba Kabir Yusuf, Kuma in Sha Allah zamu hada hannu da wannan Gidauniyar domin mu kawowa Masarautar Gaya Dama jihar Kano ci gaba.

An Kuma: Wani Dan majalisar dokokin Kano ya fice daga Kwankwasiyya

A kokarinsa na ganin ya tallafawa al’umma ko a kwanakin baya ma sai da Alhaji Najashi ya kai dauki ga sashen kula da hakori na Asibitin Sir. Sanusi da Kuma gyaran kwatoci a cikin garin gaya

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...