Zargin cin zarafi: An bukaci Gwamnan Kano ya kori kwamishiniyar jin kai

Date:

Ƙungiyar Likitoci ta ƙasa reshen jihar Kano ta yi kira ga Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya gaggauta korar Kwamishiniyar Jin Kai da Walwalara Jama’a ta jihar Hajiya Amina Abdullahi wato Amina HOD nan da awanni 48 bisa zarginta da cin zarafin wata likita.

Shugaban Kungiyar Dr. Abdurrahman Ali ya shaida wa Freedom Radio cewa suna zargin Kwamishiniyar da cin zarafin wata likita Dr. Nusaiba Mahmud a lokacin da take tsaka da aikinta a sashen bada agajin gaggawa na ɓangaren yara na Asibitin Murtala a ranar Jumu’ar da ta gabata.

Talla

A wani bidiyo da likitar ta fitar ita ma ta bayyana yadda ta sha da ƙyar inda ta ce, Kwamishiniyar ta haƙiƙi ce tana iƙrarin cewa koda ita ƴar Gwamnan Kano Engr. Abba Kabir Yusuf ce to sai ta ɗanɗana kuɗarta.

An Kuma: Wani Dan Majalisar NNPP Kano ya sake ficewa daga Kwankwasiyya

Game da wannan zargi Freedom Radio ta tuntubi Kwamishiniyar Jin Kan ta Kano Hajiya Amina HOD amma koda aka soma yi mata bayani ta wayar tarho sai ta kashe wayar, daga nan muka sake kiranta amma an saka wayar a ‘Forward”, hakan ce ta sa muka aika mata da sakonnin kar-ta-kwana amma har kawo lokacin da muke hada wannan rahoton bata amsa ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...