NNPP Ta Lashe Zaɓen Ƙananan Hukumomin Kano Baki Ɗaya

Date:

 

 

Jam’iyyar NNPP a Jihar Kano, ta lashe kujerun shugabancin ƙananan hukumomi 44 da kansiloli 484 a zaɓen ƙananan hukumomi da aka gudanar a ranar Asabar.

Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Jihar Kano (KANSIEC) ce, ta ayyana jam’iyyar a matsayin wadda ta lashe zaɓen gaba ɗaya.

Talla

Shugaban KANSIEC, Farfesa Sani Lawan Malunfashi ne, ya sanar da hakan da yammacin ranar Asabar.

Ya bayyana cewa KANSIEC ta gudanar da aikinta na gudanar zaɓen ƙananan hukumomi a Jihar Kano.

A cewarsa, an gudanar da zaɓen cikin lumana da nasara.

Za mu hada kai da sabbin Shugabannin kananan hukumomi don ciyar da Kano gaba – Gwamna Abba

Ya gode wa hukumomin tsaro, kafofin yaɗa labarai, shugabannin jam’iyyu da al’umma, tare da ƙungiyoyin matasa da mata da suka bayar da goyon baya ga tsarin dimokuraɗiyya.

Ya kuma mika godiyarsa ga mutanen Jihar Kano bisa goyon bayansu na tabbatar da zaɓen ya gudana cikin lumana.

Jam’iyyu shida ne suka shiga zaɓen na ranar Asabar; AA, AAC, Accord, ADC, APM, da kuma jamiyyar NNPP.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kotu Ta Ɗage Sauraron Ƙarar DA ICPC ta Kai Shugaban Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta Ta Jihar Kano

    Babbar kotun tarayya mai lamba shida(6) dake Babban Birnin...

Kisan ɗalibai a Kano: Kwamitin Malamai da Iyayen yara na jihar ya nuna damuwarsa

Daga Abdulhamid Isah D/Z Malam Salisu Abdullahi shugaban kwamitin malamai...

Hakikanin halin da gwamnan Katsina yake ciki, bayan wani hatsari

  Rahotanni daga Katsina na cewa gwamnan jihar Katsina Dikko...

Zargin almundahana: ICPC ku fita daga harkokin Siyasar Kano – Kungiyar Ma’aikatan KANSIEC

Daga Hafsat Abdullahi Darmanawa   Kungiyar ma'akatan wucin gadi da suka...