’Yan Sanda Sun Gargaɗi Masu Shirin Yin Zanga-Zanga A Kano

Date:

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kano, ta kammala shirye-shiryenta na daƙile tashin hankalin ko wata fitina, musamman zanga-zangar da ake shirin yi a ranar 1 ga watan Oktoba.

’Yan sanda sun tura jami’ansu zuwa wurare masu muhimmanci a faɗin jihar kuma sun yi gargaɗi mazauna Kano da su ƙaurace wa fita kan tituna domin yin zanga-zanga.

Kakakin rundunar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa ne, ya bayyana hakan a ranar Litinin.

Talla

Ya ce rundunar ba za ta yarda a sake fuskantar irin tashin hankalin da aka yi a lokacin yayin zanga-zangar #EndBadGovernance ba.

“Dangane da bikin Ranar ’Yancin Kai na 1 ga watan Oktoba 2024, rundunar ta kammala dukkanin shirye-shiryen samar da isasshen tsaro kafin da kuma bayan bikin.

Rundunar ‘yansandan jihar Kano ta kama mutane 89 da ake zargi da aikata laifuka

“Saboda haka, ina kira ga duk mazauna Jihar Kano da su haɗa kai da ’yan sanda da sauran jami’an tsaro su gudanar da bikin cikin koshin lafiya, tare da bin duk la’idojin tsaro da mutunta haƙƙin wasu.

“Haka kuma, an tura jami’an tsaro zuwa wurare masu muhimmanci domin hana kowace irin barazanar dangane da zanga-zangar da ake zaton za a yi a ranar 1 ga watan Oktoba.

Talla

“Dole ne mu fahimci cewa an samu raguwar aikata laifuka sosai,” in ji Kiyawa.

Kiyawa, ya ƙara da cewa, bisa ga umarnin Sufeta-Janar na ’Yan Sanda, Kayode Adeolu Egbetokun, rundunar ta fara haɗa kai da al’umma tare da gudanar da bincike domin daƙile laifuka.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Sarkin Kano na 15 ya gana da Shugaba Tinubu kan rikicin Rimin Zakara

    Mai Martaba Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado...

Da dumi-dumi: Tinubu ya baiwa sakataren jam’iyyar APC na Kano mukami

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Sakataren jam’iyyar APC na jihar Kano,...

Gwamnatin Kano ta haramtawa yan kwangila zuwa ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar – Kwamishina

Gwamnatin kano ta ja kunnen yan kwangilar ayyukan kananan...

Iftila’i: Almajirai 17 sun kone kurmus 15, sun jikkata sanadiyya wata gobara

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Wata gobara da ta tashi ta...