Gwamnatin Bauchi Ta Ƙaddamar Da Aikin Tsaftar Muhalli A Ƙananan Hukumomin Jihar

Date:

Daga Abubakar Yakubu

 

Kwamishinan Ma’aikatar Gidaje da Muhalli na jihar Bauchi, Rt. Honarabul Ɗanlami Ahmed Kawule (Barden Arewan Bauchi), ya ƙaddamar da aikin tsaftar Muhalli a ƙananan Hukumomin Jihar Ashirin.

Barden Arewan Bauchi ya ƙaddamar da aikin ne a Unguwar Kobi, bisa cikakken goyon bayan Gwamnan Jihar Bauchi Sanata Bala Abdulkadir Muhammad, domin tabbatar da tsafta da Lafiyar al’ummar jihar.

Talla

Manufar ƙaddamar da aikin shine, tabbatar da tsafta a lungu da saƙo na jihar, Samarwa Matasa hanyar dogaro da kansu, ƙara samar da ayyukan ci-gaba, ciki harda gyaran Masallacin Unguwar Kobi, harma da gyara magudanan ruwa domin yin kandagarkin faruwar ambaliyar ruwa.

A cewar Kwamishinan, “Duba da yadda Gwamnan Bala Muhammad ya bawa tsaftar Muhallin al’umma muhimmanci, shiyasa muka himmatu wajen gudanar da irin wannan aiki akai-akai, domin ganin cewa al’umma suna yi kamar yadda aka tsara”.

Gwamnatin Bauchi ta kammala gina gidaje 2000 domin rabawa al’umma – Kwamishinan Muhalli da Gidaje

Harma ya ce manufar shirin shine, tabbatar da tsaftar Muhalli, ƙarfafawa al’umma gwuiwar tsafta ce yankunan su, samarwa Matasa guraben aiki, samar da ƙarin ayyukan ci-gaba dama yin kandagarkin faruwar ambaliyar ruwa.

A ƙarshe sanarwar da Mashawacin Gwamnan akan kafafen sada zumunta, Alhaji Nuru Abdullahi (Baban Zahra), ya aiko wa jaridar GTR Hausa ta ce, Gwamnatin jihar zata ci-gaba ƙoƙari wajen inganta lafiya da samar da kyakykyawan Muhalli ga talakawan jihar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: Tinubu ya baiwa sakataren jam’iyyar APC na Kano mukami

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Sakataren jam’iyyar APC na jihar Kano,...

Gwamnatin Kano ta haramtawa yan kwangila zuwa ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar – Kwamishina

Gwamnatin kano ta ja kunnen yan kwangilar ayyukan kananan...

Iftila’i: Almajirai 17 sun kone kurmus 15, sun jikkata sanadiyya wata gobara

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Wata gobara da ta tashi ta...

Mun gano yadda yan Bauchi ke mamaye dazukan Kano – Gwamnatin Kano

Daga Nazifi Dukawa     Gwamnatin jihar Kano ta ce ta gano...