Maulidi: Minista T Gwarzo ya bukaci al’ummar Musulmi su rika koyi da halayen Annabi S A W

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Karamin Ministan Gidaje da Raya Birane, Abdullahi Tijjani Gwarzo ya yi kira ga Musulmin Najeriya da su yi koyi da karantarwar Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama a duk harkokinsu na yau da kullum.

Ministan ya yi wannan tsokaci ne a sakonsa na murnar zagayowar watan maulidin Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam, wanda babban mai taimaka masa kan harkokin yada labarai Adamu Abdullahi ya aikowa kadaura24.

Don haka Gwarzo ya hori musulmi da su yi riko da koyarwa tare da kwaiwayon manzon Allah mai tsira da amincin Allah, yana mai cewa hakan ne zai inganta rayuwar al’umma da kuma fitar da Nigeria daga tabarbarewar tattalin arzikin da take fuskanta .

Farashin Mai: Takaddama ta barke tsakanin Ɗangote da NNPC

A cewarsa “muna murnar zagayowar ranar haihuwar fiyayyen halitta Annabi Muhammad (SAW), amma ya zama wajibi ga dukkan musulmi su yi tunani a kan kyawawan dabi’unsa da koyarwarsa tare da yin koyi da shi a dukkan harkokinmu na yau da kullum”. “Kazalika mu rika koyi da koya da halinsa na tausayi, zaman lafiya da kaunar juna,” Ministan ya kara da cewa.

Maulidi: Murtala Sule Garo ya taya al’ummar Musulmi Murnar zagayowar watan haihuwar Annabi S A W

“Ci gabanmu ya ta’allaka ne da yadda muka aiwatar da koyarwar Manzon Allah Sallallahu Alaihi wa Sallam da ke koyar da dan Adam yadda zai zauna da kowa lafiya, wajibi ne a kan musulmin Nijeriya su yi aiki bisa koyarwa da bin ka’idojin Musulunci don ci gaban al’umma kasar mu.”

Minista Gwarzo, ya kuma yi kira ga duk masu ruwa da tsaki da su sake jajircewa wajen ganin shugaba Bola Ahmad Tinubu ya kawo sauyi a kasar nan. Ya kara da cewa ma’aikatar gidaje da raya birane ta kuduri aniyar ganin kowane dan Najeriya ya samu gidaje masu rahusa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...