Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta baiwa Sarki Aminu sabon Umarni

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Wata babbar kotun jihar Kano karkashin jagorancin mai shari’a Dije Abdu Aboki, ta bayar da umarnin wucin gadi na hana Sarkin Kano na 15, Aminu Ado Bayero gyaran karamar fadar Nasarawa.

kotun ta bayar da umarnin kar a sauya ko jirkita fasalin gidan har sai ta saurari karar da kuma yanke hukunci.

Sojojin Nijeriya sun sake hallaka kasurgumin dan fashin daji a Katsina

kazalika kotun ta bayarda umarnin sadar da sarki Aminu da umarnin nata, tare da sanya ranar 2 ga Oktoba don sauraron karar da Matawallen Kano, Alhaji Ibrahim Ahmed ya shigar.

Da dumi-dumi: Gwamnatin Kano ta sake chanza ranar komawa makarantun firamari da sakandire

Idan za’a iya tunawa Sarkin na 15 ya bayyana aniyarsa ta sake gyara gidan sarki na Nasarawa, Inda har aka fitar da taswirar yadda gidan zai kasance idan an kammala gyaran.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...