Da dumi-dumi: Gwamnatin Kano ta sake chanza ranar komawa makarantun firamari da sakandire

Date:

Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa

 

Gwamnatin jihar Kano ta sake chanja ranar komawa makarantun firamari da sakandire zuwa ranar Talata 17 ga Satumba, 2024.

Yayin da daliban makarantun kwana a fadin jihar za su koma ranar Litinin 16 ga Satumba, 2024.

Wata sanarwa da daraktan wayar da kan jama’a na ma’aikatar ilimi ta jihar, Balarabe Abdullahi Kiru ya sanya wa hannu, ta ruwaito kwamishinan ilimi na jihar Alhaji Umar Haruna Doguwa yana bayyana cewa chanja ranar komawa makarantun tana da nasa da yadda gwamnatin tarayya ta ayyana ranar 16 ga watan Satumba, 2024 a matsayin ranar hutu domin bikin Mauludi.

Sojojin Nijeriya sun sake hallaka kasurgumin dan fashin daji a Katsina

“Saboda haka an chanja ranar ne domin baiwa dalibai damar gudanar da bukukuwan maulidin fiyayyen halitta Annabi Muhammad (SAW).

Sojojin Nigeria sun Kashe Ƙasurgumin Dan ta’adda da ya addabi Arewacin Nigeria

“A yayin da nake taya al’ummar Musulmi murna, ina kira gare su da su rungumi dabi’ar hakuri, sadaukarwa, da kishin kasa tare da ci gaba da yi wa jihar kano addu’a da kasa baki daya,” inji shi.

Don haka sanarwar ta bukaci iyaye da dalibai da su lura da sabuwar ranar da za a ci gaba da aiki don tabbatar da daliban sun koma makarantunsu kamar yadda aka sanya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Zargin Almundahana: ICPC zata gurfanar da shugaban hukumar zabe ta Kano da wasu mutum biyu

    Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta (ICPC)...

Dalilin da ya hana ni zuwa Kano tarbar Tinubu – Ganduje

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Tsohon shugaban jam’iyyar APC na kasa,...

Shugaban RATTAWU na Kano ya taya sabbin shugabannin kungiyar na kasa murna

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Shugaban kungiyar ma’aikatan rediyo, Talabijin da...

Dalilina na ziyartar gwamnan Kano Abba – Inuwa Waya

Daga Rahama Umar Kwaru Tsohon Wanda ya nemi Zama Dan...