Matsalar tsaron Dorayi: Sarki Sanusi II ya yi alkawarin tallafawa kwamitin tsaron unguwar

Date:

 

Mai Martaba Sarkin Kano na 16, Malam Muhammdu Sanusi II, ya yi alƙawarin taimakawa kwamitin tabbatar da tsaron unguwar Ɗorayi da kewaye domin magance matsalar tsaron da ta dade tana addabar al’ummar yankin.

Sarki Sanusi ya bayyana hakan ne a yayin da ya karɓi baƙuncin kwamitin yankin a fadarsa, inda ya ce Masarautar za ta yi dukkan mai yiwuwa wajen ganin an magance matsalar tsaron.

Haka kuma Sarki Sanusi ya ƙara da cewa, yana matuƙar tausayawa al’ummar yankunan da matsalar take damu, duba da irin illolin da hakan ke haifarwa.

Asibitin Best Choice Ya Kaddamar Da Sabuwar Na’urar Jarirai Ta (Jaundice) Irinta Ta Farko A Arewacin Najeriya

Malam Abdullahi Idris Ɗan fodiyo yana cikin iyayen kwamitin tsaron na unguwar ta Dorayi da kewaye, ya yi wa Sarkin cikakken ƙarin haske akan matsalar tsaron da ta addabi yankin wadda take neman sabauta rayuwar su.

Zaɓen Kano: NDLEA ta fitar da sakamakon yan takara 20 da aka yiwa gwajin shan kwaya

Da yake zantawa da manema labarai jim kaɗan da fitowa daga masarautar, Ɗan Fodiyo ya bayyana ƙoƙarin da masana’antun Kano suke yi musu wajen magance matsalar tsaron yankin.

A ƙarshe dukkan ɓangarorin biyu sun yi fatan samun zaman lafiya a jihar Kano dama ƙasa baki-ɗaya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...