NiMet ta bayyana jihohin da za a kwana uku ana ruwa da tsawa

Date:

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya ta yi hasashen samun tsawa da ruwan sama daga Laraba zuwa Juma’a a faΙ—in Najeriya.

A wata sanarwa kan yanayi da hukumar ta fitar ranra Talata, ta ce ana sa ran samun tsawa a wasu sassan jihohin Borno, Adamawa, Taraba, Yobe, Katsina, Sokoto da kuma Kaduna ranar Laraba.

NiMet ta ce za a kuma samu tsawa a wasu Ι“angarorin jihohoin Kano, Katsina, Kaduna, Zamfara, Kebbi da kuma Jigawa da rana da kuma yammaci.

Asibitin Best Choice Ya Kaddamar Da Sabuwar Na’urar Jarirai Ta (Jaundice) Irinta Ta Farko A Arewacin Najeriya

“A arewa ta tsakiya, ana sa ran samun tsawa a Abuja, babban birnin Ζ™asar da Nasarawa da kuma jihar Neja a ranar Laraban,” in ji NiMet.

Jerin sunayen yan takara 38 da NNPP ta tsayar a zaΙ“en shugabannin kananan hukumomin Kano

Hukumar ta Ζ™ara da cewa a yankin kudancin Ζ™asar ma za a fuskanci tsawa da ruwan sama a jihohin Oyo da Osun da Ekiti da Ogun da Ondo da Lagos da Edo da Delta da Cross River da kuma Akwa Ibom daga Laraba zuwa Juma’a.

Hukumar ta NiMet ta kuma ce za a samu iska mai Ζ™arfi kafin saukar ruwan saman a yankuna da dama, inda ta ja hankalin jama’a cewa su Ι—auki matakan kariya da hukumomi suka fitar domin kare kansu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related